Wani masani dan kasar Zimbabwe ya bayyana a jiya Laraba cewa, ziyarar da ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi ke yi yanzu haka a Afirka wata alama ce dake nuna yadda zumunci mai karfi ya dade da kulluwa a tsakaninsu.
Masanin, wanda yake babban darakta a cibiyar nazari da bincike kan al’amuran kudancin Afirka da ta kasance babban rukuni na gudanar da binciken yanki, ya kara da cewa, shekaru 35 ke nan a jere da ministocin harkokin wajen kasar Sin suke zabar Afirka a matsayin yankin da za su fara kai ziyara a kasashen waje, wadda hakan na nuna yadda Sin ke bin manufofinta ba tare da yankewa ba da kuma fayyace Afirka a matsayin babbar kawa.
- Xi Ya Jagoranci Taron Shugabannin JKS Game Da Ayyukan Tallafin Jin Kai Bayan Aukuwar Girgizar Kasa A Xizang
- Tsakanin Sin Da Afirka: Zumunta A Kafa Take
Madakufamba ya ce, a matsayin babbar kawar cinikayyar Afirka tsawon shekaru 15 a jere, kasar Sin ta ci gaba da kara yawan kasuwancin da take yi da yankin har abin ya kai dalar Amurka biliyan 282.1 a shekarar 2023.
Ya kuma ce a kwanan baya, kasar Sin ta fara aiki da manufar soke haraji baki daya a kan kayayyakin da ake shigo da su kasarta daga kasashen Afirka 33 marasa karfin tattalin arziki, inda hakan yake bunkasa cinikayya da Afirka da kuma kara yawan damammakin kasuwanci a Afirka.
Madakufamba ya jaddada cewa, muradun kasar Sin a Afirka na cin moriyar juna ne da ke bai wa ko wane bangare damar cin gajiyar kawancen da ake yi. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp