ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Chadi Ya Gana Da Wang Yi

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Chadi

Jiya Laraba 8 ga wannan wata, shugaban kasar Chadi Mahamat Idriss Deby ya gana da mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS kuma ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi a birnin N’Djamena, fadar mulkin kasar. 

Yayin ganawar tasu, shugaba Mahamat ya taya kasar Sin murnar shirya taron kolin Beijing na dandalin tattauna hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka cikin nasara, yana mai cewa, taron kolin ya ciyar da huldar dake tsakanin sassan biyu gaba yadda ya kamata. Kuma ya nuna godiya ga kasar Sin saboda a ko da yaushe kasar tana gudanar da hadin gwiwar dake tsakaninta da kasashen Afirka bisa tushen mutunta juna, da daidaito, da kuma samun moriya tare.

  • Wang Yi Zai Kai Ziyara Kasashen Namibia, Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo, Chadi Da Najeriya
  • Akwai Buƙatar MDD Ta Shigo Don Binciko Masu Ɗaukar Nauyin Ta’addanci A Nijeriya Daga Ƙetare 

Haka kuma ya ce kasar Sin tana samar da goyon baya ga ci gaban kasashen Afirka, musamman ma kasar Chadi, baya ga nuna kwazo da himma kan kiyaye adalcin duniya. Don haka, ya ce kasarsa tana son kara karfafa cudanya da kasar Sin domin cimma muradunsu tare kuma da kiyaye moriyarsu.

ADVERTISEMENT

A nasa bangare, Wang Yi ya yi tsokacin cewa, shugabannin kasashen Sin da Chadi sun daga huldar kasashensu zuwa huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare, lamarin da ya alamta cewa, hadin gwiwar dake tsakaninsu ya shiga wani sabon mataki. Kana har kullum kasar Sin tana nacewa kan manufar tsara al’amura daidai-wa-daida tsakanin kasa da kasa, kuma tana son kara karfafa hadin gwiwar dake tsakaninta da kasar Chadi, ta yadda za su ci gaba da nuna wa juna goyon baya kamar yadda suke yi a halin yanzu.

Hakazalika, ya ce kasar Sin tana fatan za ta yi kokari tare da Chadi domin aiwatar da muhimman muradun da shugabannin kasashen biyu suka cimma, tare kuma da samar da tallafi ga ci gaban kasar Chadi, da gina kyakkyawar makomar bai daya ta Sin da Afirka a sabon zamani.

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Duk dai a wannan ranar, Wang Yi ya gana da firayin ministan kasar Chadi Allah-Maye Halina, kana ya yi shawarwari da takwaransa na kasar Abderaman Koulamallah a birnin N’Djamena. (Mai fassara: Jamila)

Chadi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
Chadi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha
  • Sulaiman
    Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
  • Sulaiman
    Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

MASU ALAKA

An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha

July 6, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
Daga Birnin Sin

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Next Post
Samun Bunkasuwa Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba Ya Zama Muhimmin Aikin Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

Samun Bunkasuwa Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba Ya Zama Muhimmin Aikin Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha

An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

July 6, 2026
Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

July 6, 2026
Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

July 6, 2026
Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.