• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Ma Cikin Waɗanda Suka Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga – Gwamnatin Katsina

by Sadiq
5 months ago
in Manyan Labarai
0
Ba Ma Cikin Waɗanda Suka Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga – Gwamnatin Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Katsina, ta bayyana cewa ba ta da hannu a wani zaman sulhu da ake zargin an yi da ‘yan bindiga, duk da rahotannin da ke cewa an cimma yarjejeniyar sulhu da shugabannin ‘yan bindiga a Ƙaramar Hukumar Batsari.

Kakakin Gwamnati kuma Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’adu na Jihar Katsina, Dokta Bala Salisu ne, ya shaidawa Daily Trust cewa gwamnatin jihar ta tsaya kan matsayinta na ƙin yin sulhu da ‘yan bindiga.

  • Trump Zai Fuskanci Tirjiya A Duniya, Ba Soyayya Ba – Shehu Sani
  • Yaƙin Gaza: Falasɗinawa Sun Fara Neman ‘Yan Uwansu Da Suka Ɓace A Baraguzan Gine-gine

Duk da haka, ya ce gwamnati za ta karɓi duk wani da ya yanke shawarar ajiye makamansa.

“Ba mu da hannu a kowace yarjejeniya ta zaman lafiya.

“Matsayin gwamnati yana nan a bayyane: duk wanda ya bar tashin hankali kuma ya ajiye makamai za mu yi la’akari da shi.

Labarai Masu Nasaba

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

“Amma ba za mu nemi ‘yan bindiga don yin sulhu ba,” in ji Dokta Salisu.

Rahotanni sun ce an yi wata ganawar zaman lafiya a ranar Lahadi a ƙauyen Kofa, kusa da garin Batsari, tare da jagorancin manyan jami’an soji, DSS, sarakunan gargajiya, da mazauna yankin.

Wani mazaunin yankin da ya halarci ganawar ya ce ‘yan bindigar sun yi alƙawarin daina kai wa al’umma hare-hare.

Sannan za su saki mutanen da suka yi garkuwa da su tare da miƙa makamai.

“Sun nemi a ba su damar shiga cikin al’umma lafiya, kuma wannan zaman an ce shi ne farkon sulhun,” in ji mazaunin.

An ce manyan shugabannin ‘yan bindiga kamar Lamu Saudo, Abdulhamid Dan Da, Umar Black, da Abu Radda sun miƙa makamansu tare da sakin waɗanda suka yi garkuwa da su a yayin taron.

Majiyoyin soji sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun miƙa wuya ne sakamakon matsin lamba da hare-haren sojoji ke ci gaba da kai musu, wanda ya sa ba su da wani zaɓi illa neman zaman lafiya.

Kakakin Rundunar Sojojin ta 17, Laftanar Lawal, ya tabbatar da wannan lamari, inda ya bayyana cewa ci gaba da matsin lambar jami’an tsaro ne ya sa ‘yan bindigar suka miƙa wuya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin KatsinaSulhuYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Trump Zai Fuskanci Tirjiya A Duniya, Ba Soyayya Ba – Shehu Sani

Next Post

Matatar Dangote Ta Bai Wa Ɗalibai 473 Tallafin Karatu

Related

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano
Manyan Labarai

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

2 hours ago
Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

16 hours ago
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

19 hours ago
An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani
Manyan Labarai

An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani

23 hours ago
Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3
Manyan Labarai

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3

1 day ago
Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump
Kasashen Ketare

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

1 day ago
Next Post
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Bai Wa Ɗalibai 473 Tallafin Karatu

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

June 25, 2025
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

June 25, 2025
Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.