• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: PDP Ta Kara Tsunduma Cikin Rikicin Shugabanci

by Yusuf Shuaibu
4 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
2027: PDP Ta Kara Tsunduma Cikin Rikicin Shugabanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da alamu dai rikicin babbar jam’iyyar adawa ta PDP bai kai ga kawo karshe ba, yayin da takaddamar ta kara kamari a tsakanin kwamitin gudanarwar jam’iyyar ta kasa, inda wasu bangarori masu madafun iko guda biyu suka fitar da sanarwar manema labarai masu cin karo da juna kan wani muhimmin al’amari na jam’iyyar.

Ba da jimawa ba sai ga wani bangare a cikin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar wanda sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na kasa, Debo Ologunagba ya wakilta a wani taron manema labarai, inda ya bayyana amincewar jam’iyyar da hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke na korar Sanata Samuel Anyanwu a matsayin sakatarenta na kasa da kuma nada Sunday Kelly Enemchukwu Udeh-Okoye a madadinsa da mataimakin sakataren yada labarai na kasa, Ibrahim Abdullahi, a yayin wani taron manema labarai na daban ya bayyana cewa Sanata Anyanwu ya ci gaba da zama a mukaminsa har sai an yanke hukunci na karshe daga kotun koli.

  • Shirin Tallafinmu Ga Nijeriya A 2025 Zai Kai Ga Asalin Mabukata – Wakilin MDD
  • Nazarin CGTN: Tsauraran Manufofin Amurka Na Shan Suka

Da yake zargin Ologunagba, Abdullahi ya yi ikirarin cewa ya yi hakan ne bisa ga umarnin mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Ambasada Umar Damagum domin nada sakataren yada labarai na kasa.

A ranar 24 ga watan Disamba ne kotun daukaka kara da ke Inugu ta kori Anyanwu tare da bayyana Udeh-Okoye a matsayin sahihan sakataren jam’iyyar na kasa biyo bayan karar da aka shigar na neman tsige Sanata Anyanwu daga wannan mukami bayan ya fito takarar a jam’iyyar a watan Nuwamba a zaben Gwamnan Jihar Imo a 2023.

Udeh- Okoye wanda ya kasance tsohon shugaban matasan jam’iyyar PDP na kasa reshen kudu maso gabas ta tsayar a matsayin wanda zai maye gurbin Sanata Anyanwu, ya yi zargin cewa shi Sanata Anyanwu ya rasa mukaminsa na sakataren kasa a lokacin da ya nemi tikitin tsayawa takara tare da samun tikitin PDP a zaben gwamnan Imo.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Sai dai a lokacin da Sanata Anyanwu ya kutsa kai cikin sakatariyar jam’iyyar PDP ta kasa bisa rashin amincewa da hukuncin kotun daukaka kara, ya yi watsi da matsayin Ologunagba kan lamarin a matsayin ra’ayinsa na kashin kansa, inda ya dage cewa ya ci gaba da zama sahihan sakataren jam’iyyar PDP na kasa har sai an yanke hukuncin karshe na shari’ar daga kotun koli.

A halin da ake ciki, yayin da Sanata Anyanwu ya nace cewa, “Na daukaka kara kan hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke, kuma na shigar da kara a dakatar da aiwatar da hukuncin, har sai an warware wadannan batutuwa, na ci gaba da zama sakataren jam’iyyar na kasa,” Ologunagba, ya ci gaba da cewa Ude-Okoye ya ci gaba da zama sahihin sakataren jam’iyyar PDP na kasa bisa karfin hukuncin kotun daukaka kara.

Masu sharhi kan harkokin siyasa da masu kallon wasan kwaikwayo da ke kunno kai a jam’iyyar PDP na ganin cewa rigimar da ke tsakanin Sanata Anyanwu da Ude Okoye kan batun sakatariyar jam’iyyar na iya kai jam’iyyar ta kara tsunduma cikin rikicin shugabanci. Sun kuma kara da cewa rigingimun na iya haifar da tsangwama ga fitintinu a cikin jam’iyyar wanda zai haifar da rarrabuwar kai a cikin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar, lamarin da zai iya samar da rikici ga wasu gwamnonin jam’iyyar da kuma ‘yan majalisar dokokin kasar da tuni aka yi zargin cewa suna cikin rikicin sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

Misali, wata majiya mai tushe ta PDP ta bayyana cewa, duk da cewa hadiman Gwamna Sheriff Francis Oborebwori sun musanta batun sauya shekarsa zuwa APC, amma hakika yana matakin karshe na shirin barin PDP.

“Gaskiyar magana ita ce gwamnan ya damu da wa’adinsa na biyu, yana jin cewa jam’iyyar PDP ta shiga wani hali mara kyau, kuma ba ta da hurumin tabbatar masa wa’adi na biyu.,” inji majiyar.

An dai bayyana cewa saboda yunkurin sauya sheka da ya yi a baya-bayan nan, Gwamna Oborebwori ya kasa hakura da sukar jam’iyyar APC da shugabanninta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: PDPRikici
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda, Sun Kama Masu Safarar Makamai, Sun Ceto Mutane

Next Post

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yaba Wa BPP Kan Fayyace Gaskiya Wajen Sayen Kayayyaki

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

3 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

3 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

3 weeks ago
Next Post
Ministan Yaɗa Labarai Ya Yaba Wa BPP Kan Fayyace Gaskiya Wajen Sayen Kayayyaki

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yaba Wa BPP Kan Fayyace Gaskiya Wajen Sayen Kayayyaki

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.