• English
  • Business News
Friday, July 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: PDP Ta Kara Tsunduma Cikin Rikicin Shugabanci

by Yusuf Shuaibu
6 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
2027: PDP Ta Kara Tsunduma Cikin Rikicin Shugabanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da alamu dai rikicin babbar jam’iyyar adawa ta PDP bai kai ga kawo karshe ba, yayin da takaddamar ta kara kamari a tsakanin kwamitin gudanarwar jam’iyyar ta kasa, inda wasu bangarori masu madafun iko guda biyu suka fitar da sanarwar manema labarai masu cin karo da juna kan wani muhimmin al’amari na jam’iyyar.

Ba da jimawa ba sai ga wani bangare a cikin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar wanda sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na kasa, Debo Ologunagba ya wakilta a wani taron manema labarai, inda ya bayyana amincewar jam’iyyar da hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke na korar Sanata Samuel Anyanwu a matsayin sakatarenta na kasa da kuma nada Sunday Kelly Enemchukwu Udeh-Okoye a madadinsa da mataimakin sakataren yada labarai na kasa, Ibrahim Abdullahi, a yayin wani taron manema labarai na daban ya bayyana cewa Sanata Anyanwu ya ci gaba da zama a mukaminsa har sai an yanke hukunci na karshe daga kotun koli.

  • Shirin Tallafinmu Ga Nijeriya A 2025 Zai Kai Ga Asalin Mabukata – Wakilin MDD
  • Nazarin CGTN: Tsauraran Manufofin Amurka Na Shan Suka

Da yake zargin Ologunagba, Abdullahi ya yi ikirarin cewa ya yi hakan ne bisa ga umarnin mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Ambasada Umar Damagum domin nada sakataren yada labarai na kasa.

A ranar 24 ga watan Disamba ne kotun daukaka kara da ke Inugu ta kori Anyanwu tare da bayyana Udeh-Okoye a matsayin sahihan sakataren jam’iyyar na kasa biyo bayan karar da aka shigar na neman tsige Sanata Anyanwu daga wannan mukami bayan ya fito takarar a jam’iyyar a watan Nuwamba a zaben Gwamnan Jihar Imo a 2023.

Udeh- Okoye wanda ya kasance tsohon shugaban matasan jam’iyyar PDP na kasa reshen kudu maso gabas ta tsayar a matsayin wanda zai maye gurbin Sanata Anyanwu, ya yi zargin cewa shi Sanata Anyanwu ya rasa mukaminsa na sakataren kasa a lokacin da ya nemi tikitin tsayawa takara tare da samun tikitin PDP a zaben gwamnan Imo.

Labarai Masu Nasaba

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

Sai dai a lokacin da Sanata Anyanwu ya kutsa kai cikin sakatariyar jam’iyyar PDP ta kasa bisa rashin amincewa da hukuncin kotun daukaka kara, ya yi watsi da matsayin Ologunagba kan lamarin a matsayin ra’ayinsa na kashin kansa, inda ya dage cewa ya ci gaba da zama sahihan sakataren jam’iyyar PDP na kasa har sai an yanke hukuncin karshe na shari’ar daga kotun koli.

A halin da ake ciki, yayin da Sanata Anyanwu ya nace cewa, “Na daukaka kara kan hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke, kuma na shigar da kara a dakatar da aiwatar da hukuncin, har sai an warware wadannan batutuwa, na ci gaba da zama sakataren jam’iyyar na kasa,” Ologunagba, ya ci gaba da cewa Ude-Okoye ya ci gaba da zama sahihin sakataren jam’iyyar PDP na kasa bisa karfin hukuncin kotun daukaka kara.

Masu sharhi kan harkokin siyasa da masu kallon wasan kwaikwayo da ke kunno kai a jam’iyyar PDP na ganin cewa rigimar da ke tsakanin Sanata Anyanwu da Ude Okoye kan batun sakatariyar jam’iyyar na iya kai jam’iyyar ta kara tsunduma cikin rikicin shugabanci. Sun kuma kara da cewa rigingimun na iya haifar da tsangwama ga fitintinu a cikin jam’iyyar wanda zai haifar da rarrabuwar kai a cikin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar, lamarin da zai iya samar da rikici ga wasu gwamnonin jam’iyyar da kuma ‘yan majalisar dokokin kasar da tuni aka yi zargin cewa suna cikin rikicin sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

Misali, wata majiya mai tushe ta PDP ta bayyana cewa, duk da cewa hadiman Gwamna Sheriff Francis Oborebwori sun musanta batun sauya shekarsa zuwa APC, amma hakika yana matakin karshe na shirin barin PDP.

“Gaskiyar magana ita ce gwamnan ya damu da wa’adinsa na biyu, yana jin cewa jam’iyyar PDP ta shiga wani hali mara kyau, kuma ba ta da hurumin tabbatar masa wa’adi na biyu.,” inji majiyar.

An dai bayyana cewa saboda yunkurin sauya sheka da ya yi a baya-bayan nan, Gwamna Oborebwori ya kasa hakura da sukar jam’iyyar APC da shugabanninta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: PDPRikici
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda, Sun Kama Masu Safarar Makamai, Sun Ceto Mutane

Next Post

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yaba Wa BPP Kan Fayyace Gaskiya Wajen Sayen Kayayyaki

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

3 hours ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

4 hours ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

5 days ago
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

7 days ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

1 week ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

1 week ago
Next Post
Ministan Yaɗa Labarai Ya Yaba Wa BPP Kan Fayyace Gaskiya Wajen Sayen Kayayyaki

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yaba Wa BPP Kan Fayyace Gaskiya Wajen Sayen Kayayyaki

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.