• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

by Bilkisu Tijjani
10 months ago
Mata

Hassana Umar Sani Matashiyar daliba a bangaran sanin cututtuka a makarantar Babura da ke Jihar Jigawa, ta shawarci mata da su dage da neman ilimi da kuma neman na kansu. Hassana ta bayyana haka cikin tattaunawarsu da wakiliyarmu BILKISU TIJJANI ALKASSIM, inda ta kara da bayyana mata irin nasarorin da ta samu da kuma kalubalen da take fuskanta a rayuwar makaranta, kamar dai yadda za ku karanta. A sha karatu lafiya.

a fari za mu so sanin cikakken sunanki da tarihinki?

Suna na Hassana Umar Sani, ni haifaffiyar garin Kano ce, na yi firamare a Al’amin Nursery and Primary School, na yi sakandire dina a Key Science GSTC Kano.

Shin Hassana matar aure ce?

A’a ba ni da aure

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Malama Hassana kina da wata sana’a ne ko kuma karatun aka sa a gaba?

Eh to a gaskiya yanzu ba ni da wata sana’a, karatu na sa a gaba, ni daliba ce a makartar lafiya dake Karamar Hukumar Babura.

Me kike karanta?

A bangaran sanin cututtuka ne

Me ya ja hankalinki da har kike sha’awar wannan karatun?

Saboda ina son sanin cututtuka da maganinsu, sannan na san idan wata cuta ta kama dan’Adam na san yadda zan bollo wa maganinta, ko wacce irin cuta na san yadda za a magance ta.

Hassana baki fada mana matakin karatunki ba?

National Diploma a shekarar karshe

Wanne irin kalubale kika taba fuskanta a cikin karatunki?

Na taba fuskantar kalubale wajen wani malami da nake da tabbacin na ci jarabawarsa kuma ya kayar da ni, saboda can wani abinsa da kuma san ransa shi ya sa ya kayar da ni.

Zuwa yanzu wadanne irin nasarori kika samu?

Nasarar da na samu shi ne na koyi abin da nima zan taimaka wa wasu mutane da dama, suma su ci moriyar abin. Ina ganin wannan ba karamar nasara bace a wajena.

Wanne abu ne ya fi faranta miki rai game da karatunki?

Abin da yake farantamin rai game da karatu na shi ne ina son in ga na koyi abu kuma na iya shi sosai, wannan gaskiya ba karamin faranta min rai yake ba.

Da me kike so mutane su rika tunawa da ke?

Ina so mutane su rika tunawa da ni akan abin alkhairi na da kuma kokarina da jajircewata

Kasancewar ke dalibar lafiya ce ance akwai tsananin katatu, ta yaya kike samun gudanar da hutunki?

Ina samu na yi karatu ta hanyar rashin yawan mutane a waje, to ya fi min sauki, wato idan waje ya yi shiru to gaskiya ina saurin fahimtar karatu cikin kankanin lokaci, har na samu na dan huta.

Wace irin addu’a ce idan aka yi miki kike jin dadi?

Addu’ar ci gaba a rayuwa ta duniya da lahira, idan aka yi min wannan addu’ar gaskiya ba karamin jin dadinta nake ba.

Wanne irin goyon baya kike samu daga wajen iyaye da ‘yan uwanki?

Ina samun goyan baya daga wajen iyayena sosai ta hanyar kwarin gwiwa da kulawarsu da suke bani, na gode musu sosai.

Kawaye fa?

Eh suma suna bani shawarwari ta hanyar karatu

Me kika fi so cikin kayan sawa da kayan kwalliya?

Inason dogayen riguna sosai , kayan kwalliya kuma ni ba ma’abociyar kwalliya bace duk abin da na samu ina amfani da shi

A karshe wanne irin shawara za ki ba ‘yan uwanki mata?

Ina so ‘yan uwana mata mu dage da neman ilimi kuma mu dage da neman na kanmu. Allah ya taimake mu baki daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

October 12, 2025
tusar gaba
Adon Gari

Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?

August 31, 2025
Next Post
Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (4)

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (4)

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.