ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
Mata

Hassana Umar Sani Matashiyar daliba a bangaran sanin cututtuka a makarantar Babura da ke Jihar Jigawa, ta shawarci mata da su dage da neman ilimi da kuma neman na kansu. Hassana ta bayyana haka cikin tattaunawarsu da wakiliyarmu BILKISU TIJJANI ALKASSIM, inda ta kara da bayyana mata irin nasarorin da ta samu da kuma kalubalen da take fuskanta a rayuwar makaranta, kamar dai yadda za ku karanta. A sha karatu lafiya.

a fari za mu so sanin cikakken sunanki da tarihinki?

Suna na Hassana Umar Sani, ni haifaffiyar garin Kano ce, na yi firamare a Al’amin Nursery and Primary School, na yi sakandire dina a Key Science GSTC Kano.

ADVERTISEMENT

Shin Hassana matar aure ce?

A’a ba ni da aure

LABARAI MASU NASABA

Sirrin Mallakar Miji 

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

Malama Hassana kina da wata sana’a ne ko kuma karatun aka sa a gaba?

Eh to a gaskiya yanzu ba ni da wata sana’a, karatu na sa a gaba, ni daliba ce a makartar lafiya dake Karamar Hukumar Babura.

Me kike karanta?

A bangaran sanin cututtuka ne

Me ya ja hankalinki da har kike sha’awar wannan karatun?

Saboda ina son sanin cututtuka da maganinsu, sannan na san idan wata cuta ta kama dan’Adam na san yadda zan bollo wa maganinta, ko wacce irin cuta na san yadda za a magance ta.

Hassana baki fada mana matakin karatunki ba?

National Diploma a shekarar karshe

Wanne irin kalubale kika taba fuskanta a cikin karatunki?

Na taba fuskantar kalubale wajen wani malami da nake da tabbacin na ci jarabawarsa kuma ya kayar da ni, saboda can wani abinsa da kuma san ransa shi ya sa ya kayar da ni.

Zuwa yanzu wadanne irin nasarori kika samu?

Nasarar da na samu shi ne na koyi abin da nima zan taimaka wa wasu mutane da dama, suma su ci moriyar abin. Ina ganin wannan ba karamar nasara bace a wajena.

Wanne abu ne ya fi faranta miki rai game da karatunki?

Abin da yake farantamin rai game da karatu na shi ne ina son in ga na koyi abu kuma na iya shi sosai, wannan gaskiya ba karamin faranta min rai yake ba.

Da me kike so mutane su rika tunawa da ke?

Ina so mutane su rika tunawa da ni akan abin alkhairi na da kuma kokarina da jajircewata

Kasancewar ke dalibar lafiya ce ance akwai tsananin katatu, ta yaya kike samun gudanar da hutunki?

Ina samu na yi karatu ta hanyar rashin yawan mutane a waje, to ya fi min sauki, wato idan waje ya yi shiru to gaskiya ina saurin fahimtar karatu cikin kankanin lokaci, har na samu na dan huta.

Wace irin addu’a ce idan aka yi miki kike jin dadi?

Addu’ar ci gaba a rayuwa ta duniya da lahira, idan aka yi min wannan addu’ar gaskiya ba karamin jin dadinta nake ba.

Wanne irin goyon baya kike samu daga wajen iyaye da ‘yan uwanki?

Ina samun goyan baya daga wajen iyayena sosai ta hanyar kwarin gwiwa da kulawarsu da suke bani, na gode musu sosai.

Kawaye fa?

Eh suma suna bani shawarwari ta hanyar karatu

Me kika fi so cikin kayan sawa da kayan kwalliya?

Inason dogayen riguna sosai , kayan kwalliya kuma ni ba ma’abociyar kwalliya bace duk abin da na samu ina amfani da shi

A karshe wanne irin shawara za ki ba ‘yan uwanki mata?

Ina so ‘yan uwana mata mu dage da neman ilimi kuma mu dage da neman na kanmu. Allah ya taimake mu baki daya.

Mata
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

MASU ALAKA

Sirrin Mallakar Miji 
Adon Gari

Sirrin Mallakar Miji 

January 25, 2026
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

October 12, 2025
Next Post
Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (4)

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (4)

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.