ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
Mata

Hassana Umar Sani Matashiyar daliba a bangaran sanin cututtuka a makarantar Babura da ke Jihar Jigawa, ta shawarci mata da su dage da neman ilimi da kuma neman na kansu. Hassana ta bayyana haka cikin tattaunawarsu da wakiliyarmu BILKISU TIJJANI ALKASSIM, inda ta kara da bayyana mata irin nasarorin da ta samu da kuma kalubalen da take fuskanta a rayuwar makaranta, kamar dai yadda za ku karanta. A sha karatu lafiya.

a fari za mu so sanin cikakken sunanki da tarihinki?

Suna na Hassana Umar Sani, ni haifaffiyar garin Kano ce, na yi firamare a Al’amin Nursery and Primary School, na yi sakandire dina a Key Science GSTC Kano.

ADVERTISEMENT

Shin Hassana matar aure ce?

A’a ba ni da aure

LABARAI MASU NASABA

Sirrin Mallakar Miji 

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

Malama Hassana kina da wata sana’a ne ko kuma karatun aka sa a gaba?

Eh to a gaskiya yanzu ba ni da wata sana’a, karatu na sa a gaba, ni daliba ce a makartar lafiya dake Karamar Hukumar Babura.

Me kike karanta?

A bangaran sanin cututtuka ne

Me ya ja hankalinki da har kike sha’awar wannan karatun?

Saboda ina son sanin cututtuka da maganinsu, sannan na san idan wata cuta ta kama dan’Adam na san yadda zan bollo wa maganinta, ko wacce irin cuta na san yadda za a magance ta.

Hassana baki fada mana matakin karatunki ba?

National Diploma a shekarar karshe

Wanne irin kalubale kika taba fuskanta a cikin karatunki?

Na taba fuskantar kalubale wajen wani malami da nake da tabbacin na ci jarabawarsa kuma ya kayar da ni, saboda can wani abinsa da kuma san ransa shi ya sa ya kayar da ni.

Zuwa yanzu wadanne irin nasarori kika samu?

Nasarar da na samu shi ne na koyi abin da nima zan taimaka wa wasu mutane da dama, suma su ci moriyar abin. Ina ganin wannan ba karamar nasara bace a wajena.

Wanne abu ne ya fi faranta miki rai game da karatunki?

Abin da yake farantamin rai game da karatu na shi ne ina son in ga na koyi abu kuma na iya shi sosai, wannan gaskiya ba karamin faranta min rai yake ba.

Da me kike so mutane su rika tunawa da ke?

Ina so mutane su rika tunawa da ni akan abin alkhairi na da kuma kokarina da jajircewata

Kasancewar ke dalibar lafiya ce ance akwai tsananin katatu, ta yaya kike samun gudanar da hutunki?

Ina samu na yi karatu ta hanyar rashin yawan mutane a waje, to ya fi min sauki, wato idan waje ya yi shiru to gaskiya ina saurin fahimtar karatu cikin kankanin lokaci, har na samu na dan huta.

Wace irin addu’a ce idan aka yi miki kike jin dadi?

Addu’ar ci gaba a rayuwa ta duniya da lahira, idan aka yi min wannan addu’ar gaskiya ba karamin jin dadinta nake ba.

Wanne irin goyon baya kike samu daga wajen iyaye da ‘yan uwanki?

Ina samun goyan baya daga wajen iyayena sosai ta hanyar kwarin gwiwa da kulawarsu da suke bani, na gode musu sosai.

Kawaye fa?

Eh suma suna bani shawarwari ta hanyar karatu

Me kika fi so cikin kayan sawa da kayan kwalliya?

Inason dogayen riguna sosai , kayan kwalliya kuma ni ba ma’abociyar kwalliya bace duk abin da na samu ina amfani da shi

A karshe wanne irin shawara za ki ba ‘yan uwanki mata?

Ina so ‘yan uwana mata mu dage da neman ilimi kuma mu dage da neman na kanmu. Allah ya taimake mu baki daya.

Mata
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji

MASU ALAKA

Sirrin Mallakar Miji 
Adon Gari

Sirrin Mallakar Miji 

January 25, 2026
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

October 12, 2025
Next Post
Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (4)

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (4)

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.