ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
Mata

Hassana Umar Sani Matashiyar daliba a bangaran sanin cututtuka a makarantar Babura da ke Jihar Jigawa, ta shawarci mata da su dage da neman ilimi da kuma neman na kansu. Hassana ta bayyana haka cikin tattaunawarsu da wakiliyarmu BILKISU TIJJANI ALKASSIM, inda ta kara da bayyana mata irin nasarorin da ta samu da kuma kalubalen da take fuskanta a rayuwar makaranta, kamar dai yadda za ku karanta. A sha karatu lafiya.

a fari za mu so sanin cikakken sunanki da tarihinki?

Suna na Hassana Umar Sani, ni haifaffiyar garin Kano ce, na yi firamare a Al’amin Nursery and Primary School, na yi sakandire dina a Key Science GSTC Kano.

ADVERTISEMENT

Shin Hassana matar aure ce?

A’a ba ni da aure

LABARAI MASU NASABA

Sirrin Mallakar Miji 

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

Malama Hassana kina da wata sana’a ne ko kuma karatun aka sa a gaba?

Eh to a gaskiya yanzu ba ni da wata sana’a, karatu na sa a gaba, ni daliba ce a makartar lafiya dake Karamar Hukumar Babura.

Me kike karanta?

A bangaran sanin cututtuka ne

Me ya ja hankalinki da har kike sha’awar wannan karatun?

Saboda ina son sanin cututtuka da maganinsu, sannan na san idan wata cuta ta kama dan’Adam na san yadda zan bollo wa maganinta, ko wacce irin cuta na san yadda za a magance ta.

Hassana baki fada mana matakin karatunki ba?

National Diploma a shekarar karshe

Wanne irin kalubale kika taba fuskanta a cikin karatunki?

Na taba fuskantar kalubale wajen wani malami da nake da tabbacin na ci jarabawarsa kuma ya kayar da ni, saboda can wani abinsa da kuma san ransa shi ya sa ya kayar da ni.

Zuwa yanzu wadanne irin nasarori kika samu?

Nasarar da na samu shi ne na koyi abin da nima zan taimaka wa wasu mutane da dama, suma su ci moriyar abin. Ina ganin wannan ba karamar nasara bace a wajena.

Wanne abu ne ya fi faranta miki rai game da karatunki?

Abin da yake farantamin rai game da karatu na shi ne ina son in ga na koyi abu kuma na iya shi sosai, wannan gaskiya ba karamin faranta min rai yake ba.

Da me kike so mutane su rika tunawa da ke?

Ina so mutane su rika tunawa da ni akan abin alkhairi na da kuma kokarina da jajircewata

Kasancewar ke dalibar lafiya ce ance akwai tsananin katatu, ta yaya kike samun gudanar da hutunki?

Ina samu na yi karatu ta hanyar rashin yawan mutane a waje, to ya fi min sauki, wato idan waje ya yi shiru to gaskiya ina saurin fahimtar karatu cikin kankanin lokaci, har na samu na dan huta.

Wace irin addu’a ce idan aka yi miki kike jin dadi?

Addu’ar ci gaba a rayuwa ta duniya da lahira, idan aka yi min wannan addu’ar gaskiya ba karamin jin dadinta nake ba.

Wanne irin goyon baya kike samu daga wajen iyaye da ‘yan uwanki?

Ina samun goyan baya daga wajen iyayena sosai ta hanyar kwarin gwiwa da kulawarsu da suke bani, na gode musu sosai.

Kawaye fa?

Eh suma suna bani shawarwari ta hanyar karatu

Me kika fi so cikin kayan sawa da kayan kwalliya?

Inason dogayen riguna sosai , kayan kwalliya kuma ni ba ma’abociyar kwalliya bace duk abin da na samu ina amfani da shi

A karshe wanne irin shawara za ki ba ‘yan uwanki mata?

Ina so ‘yan uwana mata mu dage da neman ilimi kuma mu dage da neman na kanmu. Allah ya taimake mu baki daya.

Mata
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasihar Da Ya Dace Dukkan Iyaye Su Yi Wa ‘Yaƴansu Yayin  Aure?
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?

MASU ALAKA

Sirrin Mallakar Miji 
Adon Gari

Sirrin Mallakar Miji 

January 25, 2026
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

October 12, 2025
Next Post
Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (4)

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (4)

LABARAI MASU NASABA

Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.