• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro: Kawunan Gwamnonin Arewa Sun Rabu Kan Sulhu Da ‘Yan Bindiga

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
8 months ago
Tsaro

Ana samun karuwar tashin hankali a jihohin arewa maso yammacin Nijeriya, musamman a jihohin Kaduna, Zamfara, Kebbi, da Sakkwato, wanda ya sanya gwamnonin jihohin lalubo dabarbarun dakile garkuwa da mutane da farfado da zaman lafiya a jihohin nasu.

Wadannan dabarbarun da suka kunshi tattaunawar sulhu ko kin amincewa da shi, an gano ra’ayoyi daban-daban da ke nuna irin yadda ake samun rashin hadin kai a tsakanin shugabannin arewa wajen magance matsalar tsaro.

  • Yadda Jami’an Tsaro Suka Fara Gyara Wa ‘Yan Jari Bola Zama A Abuja…
  • Babban Jami’in JKS Ya Yi Kira Da A Ci Gaba Da Kawar Da Ayyuka Mara Ma’ana

Ko a ‘yan kwanakin nan, gwamnonin jihohin da lamarin ya shafa sun yi ta kokarin nemo wasu hanyoyin kawo karshen matsalar tare da ra’ayoyin kwararrun masana harkokin tsaro kan lamarin.

Gwamnonin masu ra’ayoyi daban-daban kan matsalar tsaro na ba da hujja da abun da gwamnatinsu take ganin su ne mafita da kuma kokarin da suke yi na ganin sun kare jama’ansu.

A Kaduna, Gwamna Uba Sani ya kare shirin gwamnatinsa na yin sulhu da zaman lafiya da ‘yan bindiga da suke addabar jama’a a wasu sassan jihar.

LABARAI MASU NASABA

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

Ya ce, aikin farko da ke kan kowace gwamnati shi ne kare rayukan da dukiyar jama’a tare da tabbatar da zaman lafiya. Don haka ne ya yi cikakken bayani kan shirin sulhun da aka kwashe sama da watanni shida ana yi da masu garkuwa da mutane kuma sulhun ba ta hada da bayar da ko sisi ga ‘yan bindigan ba.

Ya ce, “Ba mu ba su ko sisin kwabo ba. Ko naira daya ba mu ba su ba. Babban abun da muka sanya a gaba shi ne kare al’ummarmu da tabbatar da zaman lafiya a jihar.”

Shirin ya haifar da sakamakon mai matukar kyau. A ranar 29 ga watan Nuwamban 2024, ya amshi ‘yan bindiga dadin da suka tuba a Birnin Gwari tare da sake bude kasuwar shanu da aka rufe tsawon shekaru sakamakon matsalar rashin tsaro.

Gwamnan ya shaida cewa manya-manyan shugabannin ‘yan bindiga da dama tare da magoya bayansu sun ajiye makamai tare da rungumar zaman lafiya.

Gwamnan ya ce da ran mutum guda ya salwanta gara ya yi komai domin kare al’ummar jihar, saboda shi ne Allah zai tambaya a ranar kiyama kan yadda ake kashe rayuka a lokacin da yake mulkin jihar.

A Jihar Zamfara kuwa, sauyin gwamnati na daga cikin dalilan da suka shafi magance matsalolin tsaro a jihar.

Tsohon gwamnan jihar, Bello Matawalle ya yi ta kokarin sulhu da ‘yan fashin dajin da nufin kawo karshen garkuwa da mutane don neman kudin fansa.

Ya hakikance kan cewa sulhun ita ce hanya mafi sauki na yaki da ‘yan fashin daji kuma a ta irin wannan sulhun ya samu nasara har aka saki ‘yan mata 26. Amma, gwamnatinsa ba ta samu zarcewa ba balle ta kara shirin da ta faro.

Sai dai kuma, gwamnati mai ci a halin yanzu ta Gwamna Dauda Lawal, ta kage kai da fata cewa atafaf babu wani zancen sulhu da ‘yan fashin daji.

Gwamna Lawal ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta shiga wani sulhu da ‘yan bindiga da suke ta’addanci a jihar ba.

Gwamnan ya ce, “Har yanzu muna kan matsayarmu cewa ba za mu yi sulhu da ‘yan ta’adda ba. Gwamnatinmu ba ta da shakka ko kadan kan matakan da muke dauka wajen shawo kan matsalar tsaro da jiharmu ke fama da shi.”

A baya dai, hanyar Abuja zuwa Kaduna ya zama wani hanyar garkuwa da mutane bisa yadda masu sace mutane ke cin karensu babu babbaka, lamarin da ke jefa razani a zukatan matafiya a kowani lokaci. Amma a yanzu hanyar ta yi lafiya wanda aka dade ba a ji lamarin sace wani mutum daya ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Next Post
Gwamnati Ta Dakatar Da Daraktocin Hukumar Sufurin Jiragen Sama 5 Sa’o’i Kadan Bayan Sauke Shugabanninsu

Tinubu Ya Umarci Sojoji Su Magance Matsalar Tsaro Kafin Karshen 2025

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.