ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro: Kawunan Gwamnonin Arewa Sun Rabu Kan Sulhu Da ‘Yan Bindiga

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
1 year ago
Tsaro

Ana samun karuwar tashin hankali a jihohin arewa maso yammacin Nijeriya, musamman a jihohin Kaduna, Zamfara, Kebbi, da Sakkwato, wanda ya sanya gwamnonin jihohin lalubo dabarbarun dakile garkuwa da mutane da farfado da zaman lafiya a jihohin nasu.

Wadannan dabarbarun da suka kunshi tattaunawar sulhu ko kin amincewa da shi, an gano ra’ayoyi daban-daban da ke nuna irin yadda ake samun rashin hadin kai a tsakanin shugabannin arewa wajen magance matsalar tsaro.

  • Yadda Jami’an Tsaro Suka Fara Gyara Wa ‘Yan Jari Bola Zama A Abuja…
  • Babban Jami’in JKS Ya Yi Kira Da A Ci Gaba Da Kawar Da Ayyuka Mara Ma’ana

Ko a ‘yan kwanakin nan, gwamnonin jihohin da lamarin ya shafa sun yi ta kokarin nemo wasu hanyoyin kawo karshen matsalar tare da ra’ayoyin kwararrun masana harkokin tsaro kan lamarin.

ADVERTISEMENT

Gwamnonin masu ra’ayoyi daban-daban kan matsalar tsaro na ba da hujja da abun da gwamnatinsu take ganin su ne mafita da kuma kokarin da suke yi na ganin sun kare jama’ansu.

A Kaduna, Gwamna Uba Sani ya kare shirin gwamnatinsa na yin sulhu da zaman lafiya da ‘yan bindiga da suke addabar jama’a a wasu sassan jihar.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Ya ce, aikin farko da ke kan kowace gwamnati shi ne kare rayukan da dukiyar jama’a tare da tabbatar da zaman lafiya. Don haka ne ya yi cikakken bayani kan shirin sulhun da aka kwashe sama da watanni shida ana yi da masu garkuwa da mutane kuma sulhun ba ta hada da bayar da ko sisi ga ‘yan bindigan ba.

Ya ce, “Ba mu ba su ko sisin kwabo ba. Ko naira daya ba mu ba su ba. Babban abun da muka sanya a gaba shi ne kare al’ummarmu da tabbatar da zaman lafiya a jihar.”

Shirin ya haifar da sakamakon mai matukar kyau. A ranar 29 ga watan Nuwamban 2024, ya amshi ‘yan bindiga dadin da suka tuba a Birnin Gwari tare da sake bude kasuwar shanu da aka rufe tsawon shekaru sakamakon matsalar rashin tsaro.

Gwamnan ya shaida cewa manya-manyan shugabannin ‘yan bindiga da dama tare da magoya bayansu sun ajiye makamai tare da rungumar zaman lafiya.

Gwamnan ya ce da ran mutum guda ya salwanta gara ya yi komai domin kare al’ummar jihar, saboda shi ne Allah zai tambaya a ranar kiyama kan yadda ake kashe rayuka a lokacin da yake mulkin jihar.

A Jihar Zamfara kuwa, sauyin gwamnati na daga cikin dalilan da suka shafi magance matsalolin tsaro a jihar.

Tsohon gwamnan jihar, Bello Matawalle ya yi ta kokarin sulhu da ‘yan fashin dajin da nufin kawo karshen garkuwa da mutane don neman kudin fansa.

Ya hakikance kan cewa sulhun ita ce hanya mafi sauki na yaki da ‘yan fashin daji kuma a ta irin wannan sulhun ya samu nasara har aka saki ‘yan mata 26. Amma, gwamnatinsa ba ta samu zarcewa ba balle ta kara shirin da ta faro.

Sai dai kuma, gwamnati mai ci a halin yanzu ta Gwamna Dauda Lawal, ta kage kai da fata cewa atafaf babu wani zancen sulhu da ‘yan fashin daji.

Gwamna Lawal ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta shiga wani sulhu da ‘yan bindiga da suke ta’addanci a jihar ba.

Gwamnan ya ce, “Har yanzu muna kan matsayarmu cewa ba za mu yi sulhu da ‘yan ta’adda ba. Gwamnatinmu ba ta da shakka ko kadan kan matakan da muke dauka wajen shawo kan matsalar tsaro da jiharmu ke fama da shi.”

A baya dai, hanyar Abuja zuwa Kaduna ya zama wani hanyar garkuwa da mutane bisa yadda masu sace mutane ke cin karensu babu babbaka, lamarin da ke jefa razani a zukatan matafiya a kowani lokaci. Amma a yanzu hanyar ta yi lafiya wanda aka dade ba a ji lamarin sace wani mutum daya ba.

Tsaro
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
Tsaro
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Gwamnati Ta Dakatar Da Daraktocin Hukumar Sufurin Jiragen Sama 5 Sa’o’i Kadan Bayan Sauke Shugabanninsu

Tinubu Ya Umarci Sojoji Su Magance Matsalar Tsaro Kafin Karshen 2025

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.