ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro: Kawunan Gwamnonin Arewa Sun Rabu Kan Sulhu Da ‘Yan Bindiga

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
1 year ago
Tsaro

Ana samun karuwar tashin hankali a jihohin arewa maso yammacin Nijeriya, musamman a jihohin Kaduna, Zamfara, Kebbi, da Sakkwato, wanda ya sanya gwamnonin jihohin lalubo dabarbarun dakile garkuwa da mutane da farfado da zaman lafiya a jihohin nasu.

Wadannan dabarbarun da suka kunshi tattaunawar sulhu ko kin amincewa da shi, an gano ra’ayoyi daban-daban da ke nuna irin yadda ake samun rashin hadin kai a tsakanin shugabannin arewa wajen magance matsalar tsaro.

  • Yadda Jami’an Tsaro Suka Fara Gyara Wa ‘Yan Jari Bola Zama A Abuja…
  • Babban Jami’in JKS Ya Yi Kira Da A Ci Gaba Da Kawar Da Ayyuka Mara Ma’ana

Ko a ‘yan kwanakin nan, gwamnonin jihohin da lamarin ya shafa sun yi ta kokarin nemo wasu hanyoyin kawo karshen matsalar tare da ra’ayoyin kwararrun masana harkokin tsaro kan lamarin.

ADVERTISEMENT

Gwamnonin masu ra’ayoyi daban-daban kan matsalar tsaro na ba da hujja da abun da gwamnatinsu take ganin su ne mafita da kuma kokarin da suke yi na ganin sun kare jama’ansu.

A Kaduna, Gwamna Uba Sani ya kare shirin gwamnatinsa na yin sulhu da zaman lafiya da ‘yan bindiga da suke addabar jama’a a wasu sassan jihar.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Ya ce, aikin farko da ke kan kowace gwamnati shi ne kare rayukan da dukiyar jama’a tare da tabbatar da zaman lafiya. Don haka ne ya yi cikakken bayani kan shirin sulhun da aka kwashe sama da watanni shida ana yi da masu garkuwa da mutane kuma sulhun ba ta hada da bayar da ko sisi ga ‘yan bindigan ba.

Ya ce, “Ba mu ba su ko sisin kwabo ba. Ko naira daya ba mu ba su ba. Babban abun da muka sanya a gaba shi ne kare al’ummarmu da tabbatar da zaman lafiya a jihar.”

Shirin ya haifar da sakamakon mai matukar kyau. A ranar 29 ga watan Nuwamban 2024, ya amshi ‘yan bindiga dadin da suka tuba a Birnin Gwari tare da sake bude kasuwar shanu da aka rufe tsawon shekaru sakamakon matsalar rashin tsaro.

Gwamnan ya shaida cewa manya-manyan shugabannin ‘yan bindiga da dama tare da magoya bayansu sun ajiye makamai tare da rungumar zaman lafiya.

Gwamnan ya ce da ran mutum guda ya salwanta gara ya yi komai domin kare al’ummar jihar, saboda shi ne Allah zai tambaya a ranar kiyama kan yadda ake kashe rayuka a lokacin da yake mulkin jihar.

A Jihar Zamfara kuwa, sauyin gwamnati na daga cikin dalilan da suka shafi magance matsalolin tsaro a jihar.

Tsohon gwamnan jihar, Bello Matawalle ya yi ta kokarin sulhu da ‘yan fashin dajin da nufin kawo karshen garkuwa da mutane don neman kudin fansa.

Ya hakikance kan cewa sulhun ita ce hanya mafi sauki na yaki da ‘yan fashin daji kuma a ta irin wannan sulhun ya samu nasara har aka saki ‘yan mata 26. Amma, gwamnatinsa ba ta samu zarcewa ba balle ta kara shirin da ta faro.

Sai dai kuma, gwamnati mai ci a halin yanzu ta Gwamna Dauda Lawal, ta kage kai da fata cewa atafaf babu wani zancen sulhu da ‘yan fashin daji.

Gwamna Lawal ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta shiga wani sulhu da ‘yan bindiga da suke ta’addanci a jihar ba.

Gwamnan ya ce, “Har yanzu muna kan matsayarmu cewa ba za mu yi sulhu da ‘yan ta’adda ba. Gwamnatinmu ba ta da shakka ko kadan kan matakan da muke dauka wajen shawo kan matsalar tsaro da jiharmu ke fama da shi.”

A baya dai, hanyar Abuja zuwa Kaduna ya zama wani hanyar garkuwa da mutane bisa yadda masu sace mutane ke cin karensu babu babbaka, lamarin da ke jefa razani a zukatan matafiya a kowani lokaci. Amma a yanzu hanyar ta yi lafiya wanda aka dade ba a ji lamarin sace wani mutum daya ba.

Tsaro
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
Tsaro
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

MASU ALAKA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
Labarai

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Gwamnati Ta Dakatar Da Daraktocin Hukumar Sufurin Jiragen Sama 5 Sa’o’i Kadan Bayan Sauke Shugabanninsu

Tinubu Ya Umarci Sojoji Su Magance Matsalar Tsaro Kafin Karshen 2025

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.