ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro: Kawunan Gwamnonin Arewa Sun Rabu Kan Sulhu Da ‘Yan Bindiga

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
2 years ago
Tsaro

Ana samun karuwar tashin hankali a jihohin arewa maso yammacin Nijeriya, musamman a jihohin Kaduna, Zamfara, Kebbi, da Sakkwato, wanda ya sanya gwamnonin jihohin lalubo dabarbarun dakile garkuwa da mutane da farfado da zaman lafiya a jihohin nasu.

Wadannan dabarbarun da suka kunshi tattaunawar sulhu ko kin amincewa da shi, an gano ra’ayoyi daban-daban da ke nuna irin yadda ake samun rashin hadin kai a tsakanin shugabannin arewa wajen magance matsalar tsaro.

  • Yadda Jami’an Tsaro Suka Fara Gyara Wa ‘Yan Jari Bola Zama A Abuja…
  • Babban Jami’in JKS Ya Yi Kira Da A Ci Gaba Da Kawar Da Ayyuka Mara Ma’ana

Ko a ‘yan kwanakin nan, gwamnonin jihohin da lamarin ya shafa sun yi ta kokarin nemo wasu hanyoyin kawo karshen matsalar tare da ra’ayoyin kwararrun masana harkokin tsaro kan lamarin.

ADVERTISEMENT

Gwamnonin masu ra’ayoyi daban-daban kan matsalar tsaro na ba da hujja da abun da gwamnatinsu take ganin su ne mafita da kuma kokarin da suke yi na ganin sun kare jama’ansu.

A Kaduna, Gwamna Uba Sani ya kare shirin gwamnatinsa na yin sulhu da zaman lafiya da ‘yan bindiga da suke addabar jama’a a wasu sassan jihar.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Ya ce, aikin farko da ke kan kowace gwamnati shi ne kare rayukan da dukiyar jama’a tare da tabbatar da zaman lafiya. Don haka ne ya yi cikakken bayani kan shirin sulhun da aka kwashe sama da watanni shida ana yi da masu garkuwa da mutane kuma sulhun ba ta hada da bayar da ko sisi ga ‘yan bindigan ba.

Ya ce, “Ba mu ba su ko sisin kwabo ba. Ko naira daya ba mu ba su ba. Babban abun da muka sanya a gaba shi ne kare al’ummarmu da tabbatar da zaman lafiya a jihar.”

Shirin ya haifar da sakamakon mai matukar kyau. A ranar 29 ga watan Nuwamban 2024, ya amshi ‘yan bindiga dadin da suka tuba a Birnin Gwari tare da sake bude kasuwar shanu da aka rufe tsawon shekaru sakamakon matsalar rashin tsaro.

Gwamnan ya shaida cewa manya-manyan shugabannin ‘yan bindiga da dama tare da magoya bayansu sun ajiye makamai tare da rungumar zaman lafiya.

Gwamnan ya ce da ran mutum guda ya salwanta gara ya yi komai domin kare al’ummar jihar, saboda shi ne Allah zai tambaya a ranar kiyama kan yadda ake kashe rayuka a lokacin da yake mulkin jihar.

A Jihar Zamfara kuwa, sauyin gwamnati na daga cikin dalilan da suka shafi magance matsalolin tsaro a jihar.

Tsohon gwamnan jihar, Bello Matawalle ya yi ta kokarin sulhu da ‘yan fashin dajin da nufin kawo karshen garkuwa da mutane don neman kudin fansa.

Ya hakikance kan cewa sulhun ita ce hanya mafi sauki na yaki da ‘yan fashin daji kuma a ta irin wannan sulhun ya samu nasara har aka saki ‘yan mata 26. Amma, gwamnatinsa ba ta samu zarcewa ba balle ta kara shirin da ta faro.

Sai dai kuma, gwamnati mai ci a halin yanzu ta Gwamna Dauda Lawal, ta kage kai da fata cewa atafaf babu wani zancen sulhu da ‘yan fashin daji.

Gwamna Lawal ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta shiga wani sulhu da ‘yan bindiga da suke ta’addanci a jihar ba.

Gwamnan ya ce, “Har yanzu muna kan matsayarmu cewa ba za mu yi sulhu da ‘yan ta’adda ba. Gwamnatinmu ba ta da shakka ko kadan kan matakan da muke dauka wajen shawo kan matsalar tsaro da jiharmu ke fama da shi.”

A baya dai, hanyar Abuja zuwa Kaduna ya zama wani hanyar garkuwa da mutane bisa yadda masu sace mutane ke cin karensu babu babbaka, lamarin da ke jefa razani a zukatan matafiya a kowani lokaci. Amma a yanzu hanyar ta yi lafiya wanda aka dade ba a ji lamarin sace wani mutum daya ba.

Tsaro
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
Tsaro
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
  • Sulaiman
    Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya
  • Sulaiman
    Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta
  • Sulaiman
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

MASU ALAKA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Tsaro
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Next Post
Gwamnati Ta Dakatar Da Daraktocin Hukumar Sufurin Jiragen Sama 5 Sa’o’i Kadan Bayan Sauke Shugabanninsu

Tinubu Ya Umarci Sojoji Su Magance Matsalar Tsaro Kafin Karshen 2025

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Tsaro

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Tsaro

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.