• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Cafke Dillalan Makamai A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
Makamai

Hukumar Kula Da Shige Da Fice ta kasa (NIS) ta ayyana cewa jami’anta sun cafke wasu mutane da ake zargin dillalan makamai ne a kan iyakar a Mfum da ke kan iyakar Nijeriya da Kamaru. 

Garin Mfum wanda yake karamar hukumar Ikom a Jihar Kuros Riba ya kasance cibiyar kasuwanci da ‘yan kasuwa na duniya ke yada zango yayin da suke safarar kayan abinci , man fetur da sauransu ta motoci zuwa kasar Kamaru.

  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne
  • 2023: Lawan Da Akpabio Ba Su Cikin ‘Yan Takarar Sanata – INEC

Kwanturolan NIS mai kula da iyakar kasa ta Mfum, CI Ndubuisi Eneregbu ya yi bayanin cafke mutanen a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a ranar Lahadi .

Eneregbu ya bayyana cewa mutum uku da aka cafke sun hada da ‘Yan Nijeriya biyu da kuma wani bakonhaure dan Kamaru wanda ya amsa cewa shi mamba ne na kungiyar ‘yan aware ta Ambazonia. An dai cafke su ne a kan babura dauke da bindigogi da albarusai.

“An cafke mutanen da ake zargin ne dauke da wata jaka da aka sa kananan bindigogi biyu da albarusai guda uku da wasu kayan tsafi da kuma waya kirar TECNO.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

“An mika mutanen da makaman da aka cafke su da su ga ofishin ‘yansanda na yankin Etung domin ci gaba da bincike. Dangane da kokarin da NIS take yi na tsaurara tsaron iyakokin kasa kuwa, Kwanturolan ya ce hukumar ta kirkiro da gudanar da taro a kai a kai tare da sarakunan dukkan garuruwan da ke kan iyaka domin samun nasara.

“Muna da kyakkyawar alaka a tsakaninmu da al’ummomin da ke iyakokin kasa . Mun gudanar da tarurruka daban-daban da al’ummomin tare da sauran humomin tsaro. A lokacin da na kama aiki a nan yankin , abin da na fara yi shi ne ziyarar dukkan sarakunan yankunan da ke karkashin kulawar ofishinmu.

“Abin da ya sa muka yi haka kuwa shi ne mun fahimci cewa akwai bukatar kyautata alaka a tsakanin jami’an tsaro da al’ummomi. Babu wata hukumar tsaro da za ta bugi kirji ta ce za ta iya yaki da matsalar tsaro ita kadai ba tare da goyon bayan al’umma ba.

“A shirye muke mu tabbatar da tsaro a kan iyaka tare da tsaftace ta daga masu yin zangon kasa ga tattalin arziki. Idan ka leka Mbok ko Yahe da sauran garuruwa na iyaka duk za ka tarar da jami’anmu a wurin” ya bayyana.

Tuni dai Shugaban NIS , CGI Isah Idris Jere ya yaba wa jami’an da suka yi nasarar cafke mutanen kana ya hore su su kara azama domin tabbatar da sauke nauyin da kasa ta dora musu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Next Post
Masarautar Mubi Da Kyakkyawan Shugabancin Sarki Alhaji Abubakar Isa Ahmadu

Masarautar Mubi Da Kyakkyawan Shugabancin Sarki Alhaji Abubakar Isa Ahmadu

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.