• Leadership Hausa
Thursday, March 23, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Cafke Dillalan Makamai A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

by Abdulrazaq Yahuza
7 months ago
in Labarai
0
NIS Ta Cafke Dillalan Makamai A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula Da Shige Da Fice ta kasa (NIS) ta ayyana cewa jami’anta sun cafke wasu mutane da ake zargin dillalan makamai ne a kan iyakar a Mfum da ke kan iyakar Nijeriya da Kamaru. 

Garin Mfum wanda yake karamar hukumar Ikom a Jihar Kuros Riba ya kasance cibiyar kasuwanci da ‘yan kasuwa na duniya ke yada zango yayin da suke safarar kayan abinci , man fetur da sauransu ta motoci zuwa kasar Kamaru.

  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne
  • 2023: Lawan Da Akpabio Ba Su Cikin ‘Yan Takarar Sanata – INEC

Kwanturolan NIS mai kula da iyakar kasa ta Mfum, CI Ndubuisi Eneregbu ya yi bayanin cafke mutanen a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a ranar Lahadi .

Eneregbu ya bayyana cewa mutum uku da aka cafke sun hada da ‘Yan Nijeriya biyu da kuma wani bakonhaure dan Kamaru wanda ya amsa cewa shi mamba ne na kungiyar ‘yan aware ta Ambazonia. An dai cafke su ne a kan babura dauke da bindigogi da albarusai.

“An cafke mutanen da ake zargin ne dauke da wata jaka da aka sa kananan bindigogi biyu da albarusai guda uku da wasu kayan tsafi da kuma waya kirar TECNO.

Labarai Masu Nasaba

Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Aiki Kafin Ranar 29 Ga Mayu

“An mika mutanen da makaman da aka cafke su da su ga ofishin ‘yansanda na yankin Etung domin ci gaba da bincike. Dangane da kokarin da NIS take yi na tsaurara tsaron iyakokin kasa kuwa, Kwanturolan ya ce hukumar ta kirkiro da gudanar da taro a kai a kai tare da sarakunan dukkan garuruwan da ke kan iyaka domin samun nasara.

“Muna da kyakkyawar alaka a tsakaninmu da al’ummomin da ke iyakokin kasa . Mun gudanar da tarurruka daban-daban da al’ummomin tare da sauran humomin tsaro. A lokacin da na kama aiki a nan yankin , abin da na fara yi shi ne ziyarar dukkan sarakunan yankunan da ke karkashin kulawar ofishinmu.

“Abin da ya sa muka yi haka kuwa shi ne mun fahimci cewa akwai bukatar kyautata alaka a tsakanin jami’an tsaro da al’ummomi. Babu wata hukumar tsaro da za ta bugi kirji ta ce za ta iya yaki da matsalar tsaro ita kadai ba tare da goyon bayan al’umma ba.

“A shirye muke mu tabbatar da tsaro a kan iyaka tare da tsaftace ta daga masu yin zangon kasa ga tattalin arziki. Idan ka leka Mbok ko Yahe da sauran garuruwa na iyaka duk za ka tarar da jami’anmu a wurin” ya bayyana.

Tuni dai Shugaban NIS , CGI Isah Idris Jere ya yaba wa jami’an da suka yi nasarar cafke mutanen kana ya hore su su kara azama domin tabbatar da sauke nauyin da kasa ta dora musu.

Tags: Bata GariDillalaiHukumaKamaruMakamaiMasu LaifiNIS
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wike Ga Atiku : Kar Ka Zarge Ni In Ka Fadi A Zabe

Next Post

Masarautar Mubi Da Kyakkyawan Shugabancin Sarki Alhaji Abubakar Isa Ahmadu

Related

Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara
Manyan Labarai

Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

23 seconds ago
Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Aiki Kafin Ranar 29 Ga Mayu
Manyan Labarai

Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Aiki Kafin Ranar 29 Ga Mayu

32 mins ago
NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Saboda Karancin Kudi A Nijeriya
Manyan Labarai

NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Saboda Karancin Kudi A Nijeriya

3 hours ago
FEC Ta Amince Da Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Wajen Gina Barikin Jami’an NDLEA
Labarai

FEC Ta Amince Da Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Wajen Gina Barikin Jami’an NDLEA

4 hours ago
Mata Magoya Bayan PDP Na Zanga-Zangar Watsi Da Sakamakon Zaben Gwamnan Kaduna
Labarai

Mata Magoya Bayan PDP Na Zanga-Zangar Watsi Da Sakamakon Zaben Gwamnan Kaduna

6 hours ago
DSS Ce Abokiyar Hamayyar Mu A Jihar Kano Ba APC Ba – NNPP
Labarai

NNPP Ta Zargi Gwamnatin Ganduje Da Kai Hare-Hare Kan Mazauna Kano

6 hours ago
Next Post
Masarautar Mubi Da Kyakkyawan Shugabancin Sarki Alhaji Abubakar Isa Ahmadu

Masarautar Mubi Da Kyakkyawan Shugabancin Sarki Alhaji Abubakar Isa Ahmadu

LABARAI MASU NASABA

Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

March 23, 2023
Siyasantar Da Batun Gano Asalin COVID-19 Dabara Ce Ta Boye Gaskiya

Siyasantar Da Batun Gano Asalin COVID-19 Dabara Ce Ta Boye Gaskiya

March 23, 2023
Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Aiki Kafin Ranar 29 Ga Mayu

Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Aiki Kafin Ranar 29 Ga Mayu

March 23, 2023
Ina So A Ko’ina A Ji Hikima Da Fasaharmu – Yusuf King

Ina So A Ko’ina A Ji Hikima Da Fasaharmu – Yusuf King

March 23, 2023
Hadin Gwiwar Sin Da Rasha Na Da Muhimmanci Sosai Ga Duniya

Hadin Gwiwar Sin Da Rasha Na Da Muhimmanci Sosai Ga Duniya

March 23, 2023
Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumin Gobe A Wasu Birane

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumin Gobe A Wasu Birane

March 23, 2023
Gyare-gyare Su Kan Faru Ne Bisa Sauyawar Tunanin Mutum

Gyare-gyare Su Kan Faru Ne Bisa Sauyawar Tunanin Mutum

March 23, 2023
NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Saboda Karancin Kudi A Nijeriya

NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Saboda Karancin Kudi A Nijeriya

March 23, 2023
FEC Ta Amince Da Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Wajen Gina Barikin Jami’an NDLEA

FEC Ta Amince Da Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Wajen Gina Barikin Jami’an NDLEA

March 23, 2023
Mata Magoya Bayan PDP Na Zanga-Zangar Watsi Da Sakamakon Zaben Gwamnan Kaduna

Mata Magoya Bayan PDP Na Zanga-Zangar Watsi Da Sakamakon Zaben Gwamnan Kaduna

March 23, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.