• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Sana’ar Kamun Kifi Sun Koka Kan Ƙarancin Kuɗaɗen Shiga A Taraba

by Abubakar Abba
3 months ago
in Labarai
0
Masu Sana’ar Kamun Kifi Sun Koka Kan Ƙarancin Kuɗaɗen Shiga A Taraba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗaruruwan masu sana’ar kamun Kifi a Jihar Taraba, sun koka kan raguwar samun kudaden shiga, sakamakon rashin samun wadatattun Kifayen da suke kamawa.

Wani bincike ya nuna cewa, a wasu shekarun baya; a kullum masu sana’ar na samun kudaden shiga daga kimanin Naira 10,000 zuwa Naira 20,000, amma yanzu sai da kyar suke iya samun Naira 10,000 a kullum.

  • Gwamnatin Kebbl Ta Dage Bikin Kamun Kifi Karo Na 61 Na Argungu Har zuwa Shekarar 2026
  • Shugaban Ghana Ya Kaddamar Da Tashar Ruwa Ta Kamun Kifi Wadda Kamfanin Sin Ya Tallafa Wajen Gina Ta

Wasu rahotanni sun nuna cewa, sama da shekarun da suka gabata, kamun Kifi na kara raguwa, wanda hakan ya tilasta wasu masu sana’ar komawa yin noma da kuma kama wasu sana’oin daban, don ci gaba da kula da rayuwarsu.

Kazalika, masu sana’ar da suka dogara kan sana’ar a kanannan hukumomi 12 na jihar, kudaden shigar da suke samu na kara raguwa.

Bincike ya nuna cewa, ana samun raguwar kamun Kifin ne, bisa abubawa da dama da suka hada da; amfani da wasu sinadaran kamun Kifin ba bisa ka’ida ba, sauyin yanayi da sauransu, wanda hakan ya haifar da raguwar yawan Kifi a Koguna.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

daya daga cikin masu sana’ar a yankin Yashin Tuwo a karamar Hukumar Karim-Lamido a jihar, Mallam Dauda Adamu, ya tabbatar da wannan kalubalen da masu sana’ar ke fuskanta a jihar, inda ya sanar da cewa, lamarin ya tilasta wasu masu sana’ar rungumar aikin noma da kama wasu sana’oin daban, domin samun kudaden shiga.

“A baya masu sana’ar a kullum suna samun kudaden shiga masu yawan gaske, sai dai; saboda raguwar Kifin a Koguna, kudaden shigar da suke samu sun ragu”, in ji Dauda.

Wani jami’i a Ma’aikatar Aikin Gona ta Jihar, wanda bai bukaci a ambaci sunansa ba, ya tabbatar da wannan raguwa ta Kifin a Kogunan jihar.

Kazalika, Mallam Dauda ya alakanta wannan kalubalen kan irin yanayin kamun Kifin da masu sana’ar ke yi, samun sauyin yanayi da kuma yin amfani da wasu sinadaran kamun Kifin da masu sana’ar ke yi a jihar, wadanda ya ce, su ne manyan ummul haba’isin matsalar da ta shafi fannin.

Ya bayyana cewa, za a iya magance wannan matsalar, a kwanakin baya; Ma’ikatar Aikin Gona ta jihar, ta kaddamar da gangamin ilimantar da kan masu sana’ar kamun Kifin a jihar, musamman kan kamun Kifin ba bisa ka’ida ba.

Kazalika, Mallam Dauda ya ce; ma’aikatar ta kuma raba wa masu sana’ar kamun Kifin ingantattun Rigar kamun Kifin da kuma sauran kayan aikin kamunsa, domin daina yin kamun Kifin ba bisa ka’ida ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KifiTaraba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ɗanyen Mai Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Ƙaru A Watan Janairun 2025 –OPEC

Next Post

Binciken Ra’ayoyi Na CGTN: Watan Daya Da Dawowar Trump Mulki, Mutanen Duniya Sun Ce Da Wuya A Ce An Gamsu Da Salonsa

Related

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

14 minutes ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

1 hour ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

2 hours ago
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

3 hours ago
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata
Labarai

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

5 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

7 hours ago
Next Post
Binciken Ra’ayoyi Na CGTN: Watan Daya Da Dawowar Trump Mulki, Mutanen Duniya Sun Ce Da Wuya A Ce An Gamsu Da Salonsa

Binciken Ra’ayoyi Na CGTN: Watan Daya Da Dawowar Trump Mulki, Mutanen Duniya Sun Ce Da Wuya A Ce An Gamsu Da Salonsa

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.