ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

by Sulaiman
7 months ago
Japan

Tsohon firaministan kasar Japan Yoshihiko Noda, ya soki kalamai marasa dacewa da firaministar Japan mai ci Sanae Takaichi ta furta dangane da yankin Taiwan na Sin, yana mai bayyana kalaman nata a matsayin na wuce gona da iri, kuma masu matukar hadari.

Noda, wanda a yanzu haka ke jagorantar jami’iyyar adawa ta CDPJ, ya yi tsokacin ne a jiya Lahadi a gundumar Nagasaki, inda ya ce, Takaichi ta zarce iyaka, kuma alakar Japan da Sin ta shiga yanayi na dar-dar, kamar dai yadda kafar watsa labarai ta Kyodo ta ruwaito.

A wani ci gaban kuma, kafar gidan talabijin ta Fuji dake Japan ta zanta da shugaban sashen tsara manufofin jam’iyyar adawa ta CDPJ Satoshi Honjo, wanda a cikin tsokacinsa ya ce, kalaman da Takaichi ta furta sun nuna rashin fahimtarta ga dokokin tsaro, da karancin saninta game da matsayin yankin Taiwan ga babban yankin kasar Sin.

ADVERTISEMENT

A ranar 7 ga watan nan, yayin da take jawabi a majalisar dokokin kasarta, firaminista Takaichi ta bayyana cewa, matakin babban yankin kasar Sin na amfani da jiragen ruwan yaki, da karfin soji kan yankin Taiwan na iya zama barazana ga dorewar Japan. Ta kuma kara da cewa, bisa tanadin dokokin kasarta, dakarun kare kasa na Japan na iya aiwatar da matakan kariya na bai daya, idan har aka lura matakin na Sin na iya zama mai hadari ga dorewar Japan.

Duk da suka daga bangarori daban daban, Takaichi ta nace cewa kalaman nata sun dace da dadaddiyar matsayar gwamnatin Japan, kuma ba ta da niyyar janye su.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Ma’aikatar raya al’adu da yawon bude ido ta kasar Sin ta fitar da sanarwa a jiya Lahadi, wadda ke kira ga al’ummunta da su yi taka-tsantsan a kwanakin nan wajen zuwa yawon bude ido kasar Japan.

Game da hakan, masani a kwalejin bincike ta Nomura Takahide Kiuchi, ya bayyana a jiyan cewa, raguwar yawan Sinawa masu zuwa yawon bude ido Japan, zai haifar da raguwar GDPn kasar ta Japan da kashi 0.36%, kana hasashen yawan asarar tattalin arziki da hakan zai haifar zai kai JYE tiriliyan 2.2, kwatankwachin kudin Sin yuan biliyan 101.6.

Bayanai sun nuna cewa, kasar Sin ce babbar abokiyar ciniki mafi girma ta Japan, kasa ta biyu mafi girma wajen fitar da kayayyaki zuwa kasar, kana babban tushen shigar da kayayyaki zuwa kasar. A shekarar 2024, jimillar darajar ciniki tsakanin Sin da Japan ta kai dalar Amurka biliyan 308.3, inda yawan kudin da Sin ta kashe wajen shigo da kayayyaki daga Japan ya kai dalar Amurka biliyan 156.25.

Kididdigar hukuma mai kula da yawon bude ido ta Japan, ta nuna cewa jimillar kudin da masu yawon bude ido na Sin suka kashe a Japan a shekarar 2024 ya haura na al’ummun sauran kasashen duniya.

Manyan ’yan siyasa, da masana masu fashin baki, da kafafen watsa labarai na yankin Taiwan, sun yi Allah wadai da kalaman tayar da husuma na firaministar Japan Sanae Takaichi dangane da yankin Taiwan na Sin, suna masu bayyana kalaman nata a matsayin wadanda suka illata moriyar al’ummun Taiwan, wato mazauna yankin dake fatan wanzuwar zaman lafiya da daidaito a daukacin mashigin Taiwan.

Da yake tsokaci kan hakan, tsohon shugaban jam’iyyar Kuomintang a yankin Taiwan Ma Ying-jeou, ya ce batutuwan da suka shafi bangarori biyu na mashigin Taiwan ba sa bukatar tsoma bakin sassan waje, yana mai jaddada cewa al’ummunsu ne kadai ke da alhakin warware su. Jami’in ya kara da cewa, Sinawa na bangarorin mashigin Taiwan biyu na da basira, da ikon warware sabaninsu cikin lumana.

Shi ma a nasa tsokaci, mawallafin mujallar “Observer” Chi Hsing, cewa ya yi, a yayin mamayar dakarun Japan, al’ummun Taiwan ba su taba dakatar da nuna turjiyarsu ba. Don haka duk wani mai kaunar adalci dake Taiwan zai yi tir da kalaman na firaminista Takaichi.

Hsieh Chih-chuan, mai fashin baki kan batutuwan siyasar Taiwan, ya ce kalaman na Takaichi sun sabawa ainihin tarihi da dokokin kasa da kasa. Daga nan sai ya gargadi ’yan aware masu rajin neman ’yancin kan Taiwan, da kada su yaudari kansu bisa kalaman na Takaichi. Domin kuwa ba makawa Sin za ta kasance kasa daya dunkulalliya.(Saminu Alhassan、Amina Xu)

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Japan
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Tinubu

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba - Tinubu Ga Alƙalai 

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.