• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gajartar Amarya Tasa Ango Ya Fasa Auren Amaryarsa Ana Tsaka Da Gudanar Da Biki

by Muhammad
3 years ago
in Al'ajabi
0
Gajartar Amarya Tasa Ango Ya Fasa Auren Amaryarsa Ana Tsaka Da Gudanar Da Biki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata budurwa ’yar kasar Tunisiya da take shirin zama amarya ta rika samun sakonnin tallafi daga sassan duniya bayan an yi watsi da bikin aurenta lokaci guda saboda sukar da surukarta ta yi mata cewa ba ta gamsu da yadda kamanninta yake ba.

Aminiya ta rawaito cewa, a karshen watan jiya ne wata budurwa mai suna Lamia al-Labawi, ta wallafa labari mai ban-tausayi a shafin Facebook inda ta bayyana yadda abin da ya kamata ya zama mafi alheri a rayuwarta ya koma wani mafarki mai ban tsoro.

  • Kasar Sin Ta Mika Wasu Takardun Amincewa Da Yarjejeniyoyi Biyu Ga ILO
  • Yadda ‘Yan Bindiga Suka Hallaka Ma’aikata Hudu Da ‘Yansanda Biyu A Kamfanin Sarrafa Tasa

Ya kamata a ce an yi aurenta da angonta shekara hudu da suka wuce amma sai yanzu; an shirya komai kuma sun kashe makudan kudi don ganin komai ya tafi yadda aka tsara, amma abin da ba su yi la’akari da shi ba, shi ne furucin mahaifiyar ango.

Lamia ta ce, ba ta taba haduwa da mahaifiyar angonta ba, kuma maimakon a yi mata tarba cikin mutunci zuwa cikin danginsu, abin da ta samu a ranar aurenta shi ne munanan kalamai.

Bayan fara bikin daurin auren, baki sun hallara, surukar Lamia da wasu sun kudiri wani abu a zuciyarsu.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

A gaban kowa, surukar ta matso kusa da danta (angon) ta ba shi umarnin ya soke bikin auren, tana mai cewa amaryar “gajera ce kuma mummuna” da ba ta cancanci ta auri danta ba.

A baya hotunan Lamia ne kawai ta gani, kuma da alama ta ji takaici sosai bayan ganin amaryar ido da ido.

Cin mutuncin da uwar angon ta yi wa amaryar bai zama wani babban al’amari ba, sai dai bakin sun yi mamakin abin da angon ya yi.

Ya bi umarnin mahaifiyarsa, kuma duk rokon da mutane da yawa suka yi a wurin bikin, amma ya watsar da auran Lamia ya bar harabar bikin tare da mahaifiyarsa.

Nan da nan labarin ya bazu a shafukan sada zumunta, kuma Lamia al-Labawi ta fara samun sakonnin goyon baya daga mutanen da suke gaya mata cewa, ta dage ta kuma gane cewa angon bai cancanci yin aure ba.

“Tare da soyayya da ’yan uwantaka, ina gaya muku, ku daga kanku ku fuskanci duniya da dukkan karfinku,” Dan wasan kwaikwayo na Tunisiya, Hedi Al-Mejri, ya rubuta wa Lamia.

“Duniya tana dauke da darasi, kuma dole ne mutum ya bambance tsakanin miji da sauran maza. Ubangijina zai saka mata da alheri, insha Allahu za ta samu abu mai kyau a gaba.

“Auren Lamia darasi ne daga darussan rayuwa, kuma gaba ta fi kyau, insha Allahu,” wani mai suna Sana Cherif ya rubuta a Facebook.

Lamia al-Labawi ta fitar da wani faifan bidiyo tana gode wa kowa kan kalaman karfafa gwiwa da suka aike mata. Abin da za a iya cewa game da angon shi ne, akalla bai yi watsi da auren a kashin kansa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Mika Wasu Takardun Amincewa Da Yarjejeniyoyi Biyu Ga ILO

Next Post

An Bude Bikin Fina-finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 Na Birnin Beijing

Related

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi
Al'ajabi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

1 week ago
An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

1 month ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

1 month ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi

2 months ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Mahaifiyarsa Da Taɓarya A Bauchi

3 months ago
‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina
Al'ajabi

Wani Jami’in Ɗansanda Ya Bindige Kansa Har Lahira A Jihar Nasarawa

4 months ago
Next Post
An Bude Bikin Fina-finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 Na Birnin Beijing

An Bude Bikin Fina-finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 Na Birnin Beijing

LABARAI MASU NASABA

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Gajarta

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.