• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yan Adawa Na Kitsa Makarkashiyar Tsige Ni – Akpabio

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
8 months ago
Akpabio

Shugaban majalisar dattawa, Godswill Obot Akpabio, ya bayyana cewa wasu ‘yan siyasa daga jihohin Adamawa da Kwara da ke jam’iyyun adawa na kitsa makarkashiyar tsige shi daga mukaminsa.

Ya bayyana hakan ne lokacin da ya amshi bakoncin shugabannin kungiyoyin matasan Neja Dalta a Abuja.

  • Mutane 7 Sun Mutu, Kadarorin Miliyan 50.3 Sun Salwanta Dalilin Gobara A Kano
  • Wata Rana Za A Yi Wa Gwamnatin Tinubu Sambarka – Minista 

Ko da yake bai ambaci sunaye ba, amma maganar ta yi nuni ga tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da kuma tsohon shugaban majalisar dattawa, Abubakar Bukola Saraki wadanda suka fito daga Adamawa da Kwara, kuma a kwanakin baya ne suka fitar da sanarwar ya sauka daga shugabancin majalisar dattawa sakamakon lamarin da ya janyo cece-kuce tsakaninsa da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan.

Duk da sun san cewa dokokin majalisar dattawan da suka shafi rashin da’a, Akpabio ya koka da cewa mutanen da ake magana da su suna yin watsi da hakikanin al’amuran da gangan saboda siyasar adawa.

“Don haka lokacin da mutane suka hada kai, sai na ji muryoyi daga Adamawa da Kwara suna ihu,ana amfani da wasu matasa daga yankin kudu maso yamma wajen yin adawa ta siyasa.Ya kamata mutum ya dunga tauna magana kafin ya fade ta”, n ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Da yake jaddada cewa ya kamata mutane su fahimci cewa a matsayinsa na shugaban majalisar dattawa, ba wai shi kadai ke wakiltar mazabarsa da jam’iyyarsa ba, har ma da yankin da ba a taba rike wannan mukami ba tsawon shekaru 46 da suka gabata.Shugaban majalisar ya bukaci wadanda ke sukar sa da su yi shiru da bakinsu.

Akpabio ya bayyana cewa shugaban majalisar dattawa ba wai kansa kadai yake wakiltar ba, al’ummar yankin Neja Delta gaba daya ba yake wakilta.

A yayin da yake jawabi a kan batun samar da kujerun zama da ya shafi Natasha Akpoti-Oduaghan, wanda ya kai ga zargin cin zarafi, Shugaban Majalisar Dattawan ya jaddada cewa mutane suna ihu ne kawai ba tare da fahimtar ka’idojin da aka shimfida ba na majalisar dattawa.

Ya ce wadanda ba su san ayyukan cikin gida na majalisar dokoki ta kasa ba za su iya fahimtar abin da ya kai ga dakatar da Natasha ba.

Da yake kare matakin dakatarwar da aka yi wa Natasha Akpoti-Uduaghan na tsawon watanni shida, Akpabio ya bayyana cewa, matakin bai daya ne na daukacin majalisar ba tare da ko daya daga cikin ‘yan majalisa da ya nuna adawa da shi ba.

Shugaban majalisar ya bukace masu sukar da su daina yin sharhin da ba su sani ba game da majalisar.

Tun da farko, Shugaban Majalisar Matasan Ijaw,Jonathan Lokpobiri wanda ya jagoranci tawagar ya nuna damuwarsa game da abubuwan da ke faruwa a majalisar dattawa, ya kuma tabbatar wa Akpabio cewa mutanen Neja Delta suna mara masa baya.

Lokpobiri ya kuma nemi shugaban majalisar dattawan ya sa baki kan rikicin da ke kunno kai a Jihar Ribas, yana mai gargadin cewa za ta iya nausawa har zuwa yankin Neja Delta baki daya idan ba a yi la’akari da shi ba.

Game da yanayin da ya shafi Natasha, shugaban matasan ya nuna damuwarsu, ko da ya ce ya kamata a dauki lamarin a matsayin batun cikin gida.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya
Manyan Labarai

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro
Manyan Labarai

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi
Manyan Labarai

Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

November 3, 2025
Next Post
Jami’in Sin: Ba Za A Lamunci Ayyukan ‘Yan Aware Na “Ballewar Taiwan” Ta Ko Wace Hanya Ba

Jami’in Sin: Ba Za A Lamunci Ayyukan ‘Yan Aware Na “Ballewar Taiwan” Ta Ko Wace Hanya Ba

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.