Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa (EFCC), ta bayyana cewa ta ƙwato Naira biliyan 365.4 a shekarar 2024 tare da samun nasara kan mutane 4,111 da aka gurfanar a kotu.
Shugaban hukumar, Ola Olukayode, ya jinjina wa ma’aikatansa kan sadaukar da kai da suka yi don cimma waɗannan nasarori.
- Tattalin Arzikin Al’Ummar Kasar Sin Na Tafiya Yadda Ya Kamata A Watan Jarairu Da Fabrairu
- Ga Dukkan Alamu Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya
Ya bayyana hakan ne a wani taron kwanaki uku da hukumar ta shirya a birnin Uyo, Jihar Akwa Ibom.
Ya ce EFCC na ƙoƙarin inganta aikinta ta hanyar aiki da gaskiya da ƙwarewa domin yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin ƙasar zagon ƙasa.
A nasa jawabin, Farfesa Tonnie Iredia ya ce rashin fahimta da murɗa labarai na daga cikin matsalolin da ke hana jama’a fahimtar ainihin aikin EFCC.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp