• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

El-Rufa’i Ya Yi Kadan Ya Sa Mu Bar Jam’iyyar PDP – Sule Lamido

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
8 months ago
Lamido

Tsohon gwamnan Jihar Jigawa kuma kusa a jam’iyyar PDP, Sule Lamido ya yi watsi da kiran da tsohon gwamnan Jihar Kaduna. Malam Nasir El-Rufa’i ya yi wa shugabannin adawa da su shiga jam’iyyar SDP. Ya ce El-Rufa’i ya yi kadan ya sa su bar jam’iyyar PDP.
El-Rufa’i, wanda a kwanan nan ne ya bar jam’iyyar APC zuwa SPD, ya bukaci manyan ‘yan siyasa ciki har da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da Peter Obi su shiga jam’iyyar tare da shi.

Sai dai kuma Lamido wanda ya kasance abokin Atiku na kusa, ya soki wannan gayyatar da El-Rufa’i ya yi musu, sannan ya kalubalanci tsarin tafiyar siyasar El-Rufa’i tare da yin alkawarin ci gaba da kokarin tallafa wa al’umma.

  • Bukatar Kawo Karshen Karin Kudin Kiran Waya Da Na Data
  • Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Zama Ƴar Amshin Shata — Kwankwaso

“Idan ba rashin kunya ba, ta yaya zai iya kalle mu a PDP kuma ya ce mu shiga wata jam’iyya. PDP wadda muka gina, ta haife shi a siyasa. Ta yaya jika zai kalli kakansa ya ce masa bai son komi ba?,” in ji Lamido.

Ya kuma kalubalanci da’awar El-Rufai na cewa yana kaunar Nijeriya fiye da wasu. Shin shi nr kawai mai son Nijeriya? Kana nufin mu babu Nijeriya a cikin zukatanmu ne?.”

Lamido ya tuna kalamun El-Rufai na cewa babu dattawan siyasa a Nijeriya, amma kuma ya garzaya wurin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya saka masa albarka lokacin da zai bai APC. Ya ce idan har ya tsaya da kafafuwansa, me ya sa ya tafi wurin Buhari?

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Lamido ya kasance tsohon sakataren jam’iyyar SDP, ya sake jaddada alkawarinsa ga PDP, yana mai cewa bai ga dalilin barinsa jam’iyyar ba.

Lokacin da na kasance sakataren jam’iyyar SDP, ina El-Rufai yake? Ina Shehu Gabam, shugaban jam’iyyar na kasa na yanzu? Duk da kalubalen da PDP ke fuskanta, a nan ne aka haife shi a siyasa. Idan yana ikirarin cewa PDP ta mutu, to ya manta da asalinsa.”
Yana jaddada cewa El-Rufa’i ya samu nasara ne a siyasa ciki har da mukamin minista da ya rike sakamakon jam’iyyar PDP ne. A cewarsa, duk abin da ya mallaka a yanzu, ya samu ne ta sanadiyyar jam’iyyar PDP ne.

Lamido ya ce ya samu damar barin PDP ciki har da lokacin da jam’iyya suka yi hadaka wajen haifar APC a 2014, amma ya zabi ya ci gaba da zama a PDP. Ya ce wadanda suka bar jam’iyyar a baya sun yi haka ne saboda fushi, inda suka dunga aibata PDP, to amma yanzu me jam’iyyar APC ta yi musu?

Haka kuma, Lamido ya nanata cewa bai kamata a nemi shugabanci wajen bacin rai na kashin kai ba, shugabanci yana bukatar hakuri, juriya, yi wa al’umma hidima da kuma kasa gaba daya. Ya ce neman shugabanci ta hanyar fusata yana kasancewa ne ta kashin kai ba ta al’ummar kasa ba.

Ya yi gargadin cewa ka da a yi adawa da Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ta hanyar bukata ta kashin kai ko yin ramako. Ya ce idan manufar ita ce kawar da Tinubu kan karagar mulki, fushi ba shi ne hanya ba. Ya ce ya san yadda zai fuskanci adawa ta fusata.

Lamido ya yi kira a samar da shugabanci mai cike da adalci da kuma martaba hakkokin al’umma. Ya ce ya kamata a mayar da hankali wajen samar da shugabanci mai cike da adalci a Nijeriya maimakon nuna fushin siyasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Sin Za Ta Kara Daidaita Matakan Jawo Jarin Waje

Sin Za Ta Kara Daidaita Matakan Jawo Jarin Waje

LABARAI MASU NASABA

tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025
Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

November 4, 2025
China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.