ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Kawo Karshen Karin Kudin Kiran Waya Da Na Data

by Bello Hamza and Sulaiman
1 year ago
NCC

A kwanan baya ne, Hukumar Sadarwa ta Kasa NCC ta sahalewa Kamfanonin Sadarwa na Kasar nan yin karin kaso 50 na kudin Data da kuma na kiran wayar tafi da gidan, inda lamarin ya haifar da cecekuce a tsakain ‘yan Nijeriya, musamman talakawa da ke amfani da kafar sadarwa.

Wannan karin ya zo ne, daidai lokacin da akasarin talakawan kasar, ke ci gaba da fuskantar matsin tattalin arziki, biyo bayan tsauraran tsare-tsaren da Gwamnatin Tarayya mai ci ta kirkiro da su.

  • Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Rahoton Amurka
  • Sin Ta Mika Tallafin Wasu Jirage Marasa Matuka Na Inganta Noma Ga Kasar Zambia

Sai dai, batun ba boyayye ba ne, duba da yadda shekara da shekaru, masana’antun sadarwa a kasar, ba su iya gudanar da ayyukansu, yadda ya dace.

ADVERTISEMENT

Duk da wannan karin na farashin Data da na kiran wayar da Kamfanonin suka yi, har yanzu ba su iya gamsar da ‘yan kasar da ayyukansu, wanda hakan ke kara sanyawa ‘yan Nigeriya ke fitar da rai daga ayyukan masana’antun.

A yayin da masu kamfanonin sadawar suka hakikance cewa, dole ne ya sanya suka yi karin, musamman domin su inganta gudanar da ayyukansu da samar da kayan aiki, amma ‘yan Nijeriya da dama suna kwan-kwanton kan yadda masu kamfanonin za su yi amfani da karin kudin shigarsu, domin ainganta ayyukansu.

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

Sai dai, idan za a yiwa wadannan Kamfanonin adalci, sun jima suna yin cajin farashinsu da sauki, musamman idan aka kwatanta da sauran fannonin.

Bugu da kari, matsin tattalin azrkin kasa, hauhawan farashin kaya, cire tallafin man fetur, karin farashin makamashi, karin farashin kudin wutar lantarki,sun kara zamowa Kamfanonin sadarwar matsala wajen ci gaba da samun riba.

Kazalika, wadannan matsalolin sun kai ga har sun shafi ma’aikatan da ke aiki a wadannan Kamfanonin, duba da yadda Kamfanonin suka gaza karawa ma’aikatansu albashi.

Sai dai, Kamfanonin sadawarwa MTN, Glo, Airtelda kuma 9mobile, suna hakilon lalubo da mafita kan yanewar kiran waya da rashin gudun da Data da rashin samun sadarwa.
Masu Kamfanonin sun bayyana cewa, ‘yan Nijeriya za su ci gaba da fuskantar ingancin ayyukan Kamfanonin, matukar za a ci gaba da fuskantar matsalar wutar lantarki da lalata masu kayan aikinsu.

Kungiyr da ke bai wa Kafanonin Sadawar Lasisi ta Kasa ALTON, ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kawo dauki, domin a magance rashin ingancin ayyukan Kamfanonin a kasar.

Hukumar ta NCC ta alakanta rashin ignacin ayyukan Kamfanonin kan yadda ake lalata masu na’urorinsu a fadin kasar, musamman duba da cewa, gudanar da ingantaccen aikin Kamfanonin shi ne, ginshikin samar da sadarwa.

Kamfanonin sadawar a kasar nan na bukatar ayi masu garanbawul, kuma ya zama wajibi Hukumar NCC ta zargi Kamfanonin sadarwar, kan gazawar su ta rashin samar da ingantaccen aiki, musamman domin masu amfani da kakafen sadarwar, sun san da cewa, suna morar kudadensu.

Bugu da kari, ya zama wajibi Hukumar NCC ta mayar da hankali wajen tabbatar da cewa, ana bai wa masu amfani da kamfaninin sadarwar kariyar da ta kamata da kuma tabbatar da cewa, suna amfana da ayyukan Kamfanonin ba tare da fuskantar wata tangarda daga ayyukansu ba.

Kazaliaka, ya kamata Hukumar ta NCC ta kara mayar da hankaili wajen sanya gasa a masana’antar Sadarwar da kuma sanar da wata sabuwar kasuwa, wanda hakan zai sanya masu amfanin da Kamfanonin sadarwa a kasar za su zabi Kamfanonin sadarwar da suke ganin, za su biya masu bukatarasu, ba tare da fuskantar wata matsala.

Lokaci ya yi da Kamfanonin sadawar da ke a kasar nan, su tabbatar da cewa, suna mayarda hankali wajen bai wa masu amfani da layukan sadarwa a kasar kariyar da ta kamata, Kamfanonin su kuma tabatar da cewa, suna zuba hannun jari wajen kara inganta ayyukansu, musamman domin amfanin daukacin ‘yan Nijeriya.

Bugu da kari, yana da kyau, Kamfanonin sadarwar da ke a kasar nan, su tashi tsaye wajen lalubo da mafita kan kalubalen da masa’antar ke fuskanta, musamman domin masana;antar, ta ci gaba da dorewa.

Idan har a kasar nan, ba a dauku matakan inganta masana’antar ba, to tabbas wata rana, za ta zama sai dai Buzunta.

Kiran waya
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata
Kiran waya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026
Next Post
Yadda Azumi Yake Sa Tsoron Allah

Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.