ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Kawo Karshen Karin Kudin Kiran Waya Da Na Data

by Bello Hamza and Sulaiman
1 year ago
NCC

A kwanan baya ne, Hukumar Sadarwa ta Kasa NCC ta sahalewa Kamfanonin Sadarwa na Kasar nan yin karin kaso 50 na kudin Data da kuma na kiran wayar tafi da gidan, inda lamarin ya haifar da cecekuce a tsakain ‘yan Nijeriya, musamman talakawa da ke amfani da kafar sadarwa.

Wannan karin ya zo ne, daidai lokacin da akasarin talakawan kasar, ke ci gaba da fuskantar matsin tattalin arziki, biyo bayan tsauraran tsare-tsaren da Gwamnatin Tarayya mai ci ta kirkiro da su.

  • Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Rahoton Amurka
  • Sin Ta Mika Tallafin Wasu Jirage Marasa Matuka Na Inganta Noma Ga Kasar Zambia

Sai dai, batun ba boyayye ba ne, duba da yadda shekara da shekaru, masana’antun sadarwa a kasar, ba su iya gudanar da ayyukansu, yadda ya dace.

ADVERTISEMENT

Duk da wannan karin na farashin Data da na kiran wayar da Kamfanonin suka yi, har yanzu ba su iya gamsar da ‘yan kasar da ayyukansu, wanda hakan ke kara sanyawa ‘yan Nigeriya ke fitar da rai daga ayyukan masana’antun.

A yayin da masu kamfanonin sadawar suka hakikance cewa, dole ne ya sanya suka yi karin, musamman domin su inganta gudanar da ayyukansu da samar da kayan aiki, amma ‘yan Nijeriya da dama suna kwan-kwanton kan yadda masu kamfanonin za su yi amfani da karin kudin shigarsu, domin ainganta ayyukansu.

LABARAI MASU NASABA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

Sai dai, idan za a yiwa wadannan Kamfanonin adalci, sun jima suna yin cajin farashinsu da sauki, musamman idan aka kwatanta da sauran fannonin.

Bugu da kari, matsin tattalin azrkin kasa, hauhawan farashin kaya, cire tallafin man fetur, karin farashin makamashi, karin farashin kudin wutar lantarki,sun kara zamowa Kamfanonin sadarwar matsala wajen ci gaba da samun riba.

Kazalika, wadannan matsalolin sun kai ga har sun shafi ma’aikatan da ke aiki a wadannan Kamfanonin, duba da yadda Kamfanonin suka gaza karawa ma’aikatansu albashi.

Sai dai, Kamfanonin sadawarwa MTN, Glo, Airtelda kuma 9mobile, suna hakilon lalubo da mafita kan yanewar kiran waya da rashin gudun da Data da rashin samun sadarwa.
Masu Kamfanonin sun bayyana cewa, ‘yan Nijeriya za su ci gaba da fuskantar ingancin ayyukan Kamfanonin, matukar za a ci gaba da fuskantar matsalar wutar lantarki da lalata masu kayan aikinsu.

Kungiyr da ke bai wa Kafanonin Sadawar Lasisi ta Kasa ALTON, ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kawo dauki, domin a magance rashin ingancin ayyukan Kamfanonin a kasar.

Hukumar ta NCC ta alakanta rashin ignacin ayyukan Kamfanonin kan yadda ake lalata masu na’urorinsu a fadin kasar, musamman duba da cewa, gudanar da ingantaccen aikin Kamfanonin shi ne, ginshikin samar da sadarwa.

Kamfanonin sadawar a kasar nan na bukatar ayi masu garanbawul, kuma ya zama wajibi Hukumar NCC ta zargi Kamfanonin sadarwar, kan gazawar su ta rashin samar da ingantaccen aiki, musamman domin masu amfani da kakafen sadarwar, sun san da cewa, suna morar kudadensu.

Bugu da kari, ya zama wajibi Hukumar NCC ta mayar da hankali wajen tabbatar da cewa, ana bai wa masu amfani da kamfaninin sadarwar kariyar da ta kamata da kuma tabbatar da cewa, suna amfana da ayyukan Kamfanonin ba tare da fuskantar wata tangarda daga ayyukansu ba.

Kazaliaka, ya kamata Hukumar ta NCC ta kara mayar da hankaili wajen sanya gasa a masana’antar Sadarwar da kuma sanar da wata sabuwar kasuwa, wanda hakan zai sanya masu amfanin da Kamfanonin sadarwa a kasar za su zabi Kamfanonin sadarwar da suke ganin, za su biya masu bukatarasu, ba tare da fuskantar wata matsala.

Lokaci ya yi da Kamfanonin sadawar da ke a kasar nan, su tabbatar da cewa, suna mayarda hankali wajen bai wa masu amfani da layukan sadarwa a kasar kariyar da ta kamata, Kamfanonin su kuma tabatar da cewa, suna zuba hannun jari wajen kara inganta ayyukansu, musamman domin amfanin daukacin ‘yan Nijeriya.

Bugu da kari, yana da kyau, Kamfanonin sadarwar da ke a kasar nan, su tashi tsaye wajen lalubo da mafita kan kalubalen da masa’antar ke fuskanta, musamman domin masana;antar, ta ci gaba da dorewa.

Idan har a kasar nan, ba a dauku matakan inganta masana’antar ba, to tabbas wata rana, za ta zama sai dai Buzunta.

Kiran waya
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
Kiran waya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
Ra'ayinmu

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
Ra'ayinmu

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

July 3, 2026
sikila
Ra'ayinmu

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Next Post
Yadda Azumi Yake Sa Tsoron Allah

Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.