ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Kawo Karshen Karin Kudin Kiran Waya Da Na Data

by Bello Hamza and Sulaiman
1 year ago
NCC

A kwanan baya ne, Hukumar Sadarwa ta Kasa NCC ta sahalewa Kamfanonin Sadarwa na Kasar nan yin karin kaso 50 na kudin Data da kuma na kiran wayar tafi da gidan, inda lamarin ya haifar da cecekuce a tsakain ‘yan Nijeriya, musamman talakawa da ke amfani da kafar sadarwa.

Wannan karin ya zo ne, daidai lokacin da akasarin talakawan kasar, ke ci gaba da fuskantar matsin tattalin arziki, biyo bayan tsauraran tsare-tsaren da Gwamnatin Tarayya mai ci ta kirkiro da su.

  • Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Rahoton Amurka
  • Sin Ta Mika Tallafin Wasu Jirage Marasa Matuka Na Inganta Noma Ga Kasar Zambia

Sai dai, batun ba boyayye ba ne, duba da yadda shekara da shekaru, masana’antun sadarwa a kasar, ba su iya gudanar da ayyukansu, yadda ya dace.

ADVERTISEMENT

Duk da wannan karin na farashin Data da na kiran wayar da Kamfanonin suka yi, har yanzu ba su iya gamsar da ‘yan kasar da ayyukansu, wanda hakan ke kara sanyawa ‘yan Nigeriya ke fitar da rai daga ayyukan masana’antun.

A yayin da masu kamfanonin sadawar suka hakikance cewa, dole ne ya sanya suka yi karin, musamman domin su inganta gudanar da ayyukansu da samar da kayan aiki, amma ‘yan Nijeriya da dama suna kwan-kwanton kan yadda masu kamfanonin za su yi amfani da karin kudin shigarsu, domin ainganta ayyukansu.

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

Sai dai, idan za a yiwa wadannan Kamfanonin adalci, sun jima suna yin cajin farashinsu da sauki, musamman idan aka kwatanta da sauran fannonin.

Bugu da kari, matsin tattalin azrkin kasa, hauhawan farashin kaya, cire tallafin man fetur, karin farashin makamashi, karin farashin kudin wutar lantarki,sun kara zamowa Kamfanonin sadarwar matsala wajen ci gaba da samun riba.

Kazalika, wadannan matsalolin sun kai ga har sun shafi ma’aikatan da ke aiki a wadannan Kamfanonin, duba da yadda Kamfanonin suka gaza karawa ma’aikatansu albashi.

Sai dai, Kamfanonin sadawarwa MTN, Glo, Airtelda kuma 9mobile, suna hakilon lalubo da mafita kan yanewar kiran waya da rashin gudun da Data da rashin samun sadarwa.
Masu Kamfanonin sun bayyana cewa, ‘yan Nijeriya za su ci gaba da fuskantar ingancin ayyukan Kamfanonin, matukar za a ci gaba da fuskantar matsalar wutar lantarki da lalata masu kayan aikinsu.

Kungiyr da ke bai wa Kafanonin Sadawar Lasisi ta Kasa ALTON, ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kawo dauki, domin a magance rashin ingancin ayyukan Kamfanonin a kasar.

Hukumar ta NCC ta alakanta rashin ignacin ayyukan Kamfanonin kan yadda ake lalata masu na’urorinsu a fadin kasar, musamman duba da cewa, gudanar da ingantaccen aikin Kamfanonin shi ne, ginshikin samar da sadarwa.

Kamfanonin sadawar a kasar nan na bukatar ayi masu garanbawul, kuma ya zama wajibi Hukumar NCC ta zargi Kamfanonin sadarwar, kan gazawar su ta rashin samar da ingantaccen aiki, musamman domin masu amfani da kakafen sadarwar, sun san da cewa, suna morar kudadensu.

Bugu da kari, ya zama wajibi Hukumar NCC ta mayar da hankali wajen tabbatar da cewa, ana bai wa masu amfani da kamfaninin sadarwar kariyar da ta kamata da kuma tabbatar da cewa, suna amfana da ayyukan Kamfanonin ba tare da fuskantar wata tangarda daga ayyukansu ba.

Kazaliaka, ya kamata Hukumar ta NCC ta kara mayar da hankaili wajen sanya gasa a masana’antar Sadarwar da kuma sanar da wata sabuwar kasuwa, wanda hakan zai sanya masu amfanin da Kamfanonin sadarwa a kasar za su zabi Kamfanonin sadarwar da suke ganin, za su biya masu bukatarasu, ba tare da fuskantar wata matsala.

Lokaci ya yi da Kamfanonin sadawar da ke a kasar nan, su tabbatar da cewa, suna mayarda hankali wajen bai wa masu amfani da layukan sadarwa a kasar kariyar da ta kamata, Kamfanonin su kuma tabatar da cewa, suna zuba hannun jari wajen kara inganta ayyukansu, musamman domin amfanin daukacin ‘yan Nijeriya.

Bugu da kari, yana da kyau, Kamfanonin sadarwar da ke a kasar nan, su tashi tsaye wajen lalubo da mafita kan kalubalen da masa’antar ke fuskanta, musamman domin masana;antar, ta ci gaba da dorewa.

Idan har a kasar nan, ba a dauku matakan inganta masana’antar ba, to tabbas wata rana, za ta zama sai dai Buzunta.

Kiran waya
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja
Kiran waya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026
Next Post
Yadda Azumi Yake Sa Tsoron Allah

Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.