• English
  • Business News
Monday, June 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [19]

by Nuhu Ubale Ibrahim
3 months ago
in Addini, Bakon Marubuci, Ilimi
0
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Faidar Istigfari:

Ibnu Juzai a-Kalbi Allah Ya yi masa rahama yana cewa:

وَ أَمَّا ٱلٱسْتِغْفَارُ فَثَمَرَتُهُ ٱلٱسْتِقَامَةُ عَلَى ٱلتَّقْوَىٰ، وَ ٱلْمُحَافَظَةُ عَلَىٰ شُرُوطِ ٱلتَّوْبَةِ مَعَ إِنْكَارِ ٱلْقَلْبِ بِسَبَبِ ٱلذُّنُوبِ.

Fassara:

“ Ka ga yin istigfari, sakamakonsa shi ne tsayuwa kan taƙawa, da kiyaye sharuɗan tuba, tare da inkarin saɓo da zuciya za ta yi saboda zunuban da aka aikata” Duba Kitãbu at-Tashīlu Li’ulūmi at-Tanzil [1/65]

Labarai Masu Nasaba

Babban Al’amari Ne A Samu Ƴar Shekara 6 Ta Haddace Qur’ani A Makarantar Raudatul Jannah – Mai Sikeli

Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata Alƙur’ani – Daurawa

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [18]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [17]

Fashin Baƙi:

Wannan magana ta Ibnu Juzai al-Kalbi Allah Ya ji ƙan sa tana bayani ne a kan istigfari ( wato nema gafarar Allah) da sakamakonsa a rayuwar mutum. Domin fahimtar wannan tasa dalla-dalla, zan yi bayani a matakai uku:

Ma’anar Istigfari da Muhimmancinsa:

Istigfari na nufin neman gafarar Allah Ta’ala bisa zunubai da aka aikata. Ana yin hakan ta hanyar faɗin “Astaghfirullah” da sauran lafuzza masu kama da hakan. Allah Maɗaukakin Sarki ya yawaita umurni da a yi istigfari a cikin Alƙur’ani, kamar yadda ya ce:
” sai na ce: Ku nemi gafarar Ubangijinku, lalle Shi Ya kasance Mai ywana gafara ne” Suratu Nuh aya ta 10.

Manzon Allah (S.A.W) yana yawaita istigfari fiye da sau saba’in a rana, kamar yadda hadisi ya tabbatar da haka a cikin Sahihul Bukhari da Muslim..

Sakamakon Istigfari a Bisa Maganar Ibnu Juzai:

Ibnu Juzai yana bayani ne cewa istigfari yana da tasiri a rayuwar mai neman gafara, kuma sakamakonsa yana bayyana a cikin:

Tsayuwa Kan Taƙawa:
Taƙawa tana nufin kiyaye umarnin Allah da guje wa haninsa wato nisantar saɓa masa. Idan mutum yana neman gafarar Allah da gaske, hakan yana ƙarfafa tsoron Allah a zuciyarsa, wanda ke hana shi komawa ga zunubi. Allah Ta’ala Yana cewa:” Kuma ku tuba ga Allah gaba ɗayanku ya ku mummunai domin ku rabauta” Suratun Nur aya ta 31.

Kiyaye Sharuddan Tuba:
Tuba tana da sharuɗa guda uku, idan zunubin ba ya da alaƙa da wani bawa, to sharuɗan guda uku ne, idan kuma yana da alaƙa da wani, to sharuɗan hudu ne kamar haka:

1. Nadama bisa abin da aka aikata.
2. Barin zunubin nan take ba tare da jinkiri ba.
3. Ƙudirin kada a koma ga zunubin nan gaba.
4. Idan ya shafi wani mutum, sai a biya shi haƙƙinsa.

Idan mutum yana istigfari ba tare da kiyaye waɗannan sharuɗa ba, to istigfarinsa ba zai ba yi mass tasiri sosai ba.

Inkarin Saɓo da Zuciya:
Wannan yana nuna cewa zuciyar mai istigfari tana ƙin saɓo kuma tana jin haushin zunuban da aka aikata a baya. Wannan na nufin istigfari na gaskiya yan ƙarfafar bawa a kan aibata saɓo da jin nauyin aika shi. Hakan yana nufin istigfari yana gina halin mutumin da ya fahimci girman zunubi, kuma hakan yana hana shi sake aikata shi.

Muhimmancin Wannan Magana a Rayuwa:

Maganar Ibnu Juzai tana koyar da cewa:
• Istigfari ba kawai furuci ba ne, yana da tasiri ga zuciya da hali.
• Dole ne istigfari ya kasance tare da takawa da gujewa sabo.
• Kiyaye sharuɗan tuba yana tabbatar da cewa istigfarin mutum ya dace da shari’a.

A taƙaice, Ibnu Juzai a-Kalbi Allah Ya ji ƙan sa yana jaddada cewa istigfari na gaskiya yana haifar da tsayuwa a kan addini, da kiyaye dokokin Allah, da gujewa komawa ga zunubi. Wannan yana nufin cewa nema gafarar Allah ba wai magana ce ta fatar baki kawai ba, sai da aikin zuciya da na gaɓɓai.

Allah ya sa mu kasance cikin masu istigfari na gaskiya!


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abu Razina Nuhu Ubale PakiAl-qur'aniAlƙur’aniIbnu JuzaiRamadanTafsiriTafsirin Alƙur’aniTafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Za Ta Dauki Matakai Don Kiyaye Hakki Da Muradun Kamfanoninta

Next Post

Sallah: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Litinin Da Talata A Matsayin Hutu

Related

Babban Al’amari Ne A Samu Ƴar Shekara 6 Ta Haddace Qur’ani A Makarantar Raudatul Jannah – Mai Sikeli
Addini

Babban Al’amari Ne A Samu Ƴar Shekara 6 Ta Haddace Qur’ani A Makarantar Raudatul Jannah – Mai Sikeli

1 day ago
Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata Alƙur’ani – Daurawa
Addini

Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata Alƙur’ani – Daurawa

2 days ago
Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata
Addini

Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata

2 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

3 days ago
Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC
Ilimi

Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

1 week ago
Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 
Bakon Marubuci

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

1 week ago
Next Post
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Sallah: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Litinin Da Talata A Matsayin Hutu

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

June 23, 2025
Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

June 23, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya

June 23, 2025
Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

June 23, 2025
Gwamnan Abba Kabir Yusuf tare da Arch. Ali Hassan

Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan

June 23, 2025
2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

June 22, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

June 22, 2025
Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

June 22, 2025
Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

June 22, 2025
Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

June 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.