ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

by Abubakar Sulaiman
9 months ago
Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina ta bayar da umarnin rufe makarantu 32 na gaba da sakandare masu zaman kansu da ke aiki ba tare da lasisi ko sahalewar hukumomin da ke kula da ilimi ba a jihar.

Kwamishinan Ilimi na Manyan Makarantu, Fasaha da Sana’o’i, Dr. Muhammad Isah Kankara, ne ya bayyana hakan yayin kare kasafin kuɗin ma’aikatarsa na shekarar 2026 a gaban kwamiti ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan tsare-tsare da tattalin arziƙi, Malik Anas, a Katsina.

  • Ina Aka Kwana Batun Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Dazukan Jihar Katsina?
  • Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Dr. Kankara ya ce binciken ma’aikatar ya gano cewa da dama daga cikin makarantun masu zaman kansu suna gudanar da aiki ne ba bisa ƙa’ida ba, ba tare da cika ƙa’idojin ƙasa ba.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa wannan mataki ya zama dole domin kare ɗalibai da tabbatar da ingancin ilimi a fadin jihar.

“Bincikenmu ya nuna cewa wasu makarantun masu zaman kansu suna aiki ne ba tare da amincewar hukumomin da suka dace ba,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Kwamishinan ya amince cewa rufe makarantun ya shafi kuɗaɗen shiga na cikin gida (IGR) da ake sa ran samu a shekarar 2026, domin da yawa daga cikin makarantun da aka rufe suna taka muhimmiyar rawa wajen samar da kuɗaɗen shiga ga ma’aikatar.

“Adadin kuɗaɗen shiga zai ragu a bana saboda yawancin waɗannan makarantun da aka dakatar suna cikin waɗanda ke taimaka mana wajen samar da kuɗi. Za mu iya dawo da su ne kawai idan suka cika sharuddan da doka ta tanada,” in ji Kankara.

A yayin zaman, shugaban kwamitin kasafin kuɗi, Malik Anas, ya umarci ma’aikatar da ta gabatar da cikakken jerin makarantun da ke da lasisi da waɗanda ba su da shi, tare da hasashen kudaden shiga daga kowacce.

Dr. Kankara ya bayyana cewa ma’aikatar tana tattara bayanan da ake buƙata kuma za ta mika cikakken rahoto nan ba da jimawa ba.

Ya ƙara da cewa makarantu guda bakwai (7) kawai daga cikin 39 masu zaman kansu ne aka tabbatar da sahihancinsu kuma suna ci gaba da aiki bayan wannan rufe-rufe.

Kwamitin ya yaba wa ma’aikatar bisa tsaurara dokoki don tabbatar da bin ƙa’idoji, tare da umartar ta da ta kawo sabbin bayanai kafin kasafin shekara mai zuwa.

Katsina
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata
  • Abubakar Sulaiman
    Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

MASU ALAKA

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
Next Post
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya - TRCN

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

July 7, 2026
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.