• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arzikin Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Karin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arzikin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A halin da ake ciki yanzu haka, yanayin tattalin arzikin duniya na fuskantar guguwar rashin tabbas, a gabar da Amurka ke kara tsaurara matakan kakaba haraji kan hajojin da ake shigarwa kasar daga wasu kasashen duniya, matakan da masana tattalin arziki daga sassan kasa da kasa ke ta suka, tare da bayyana su a matsayin illa da ka iya dakile ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya, baya ga ingiza hauhawar farashi, da gurgunta tsarin cinikayyar kasa da kasa da hakan zai haifar. 

Bisa halin da ake ciki, masu masana tattalin arziki na ganin matakan nan na kakaba karin haraji da Amurka ke aiwatarwa, za su ci gaba da zama barazana ga daidaiton tattalin arzikin duniya, kuma ko da kaso kadan daga cikin su Amurka ta aiwatar, hakan na iya tauye hasashen da aka yi na ci gaban tattalin arzikin duniya, tare da haifar da hauhawar farashi a Amurka ita kanta.

  • Sallah: ’Yansanda Sun Yi Alƙawarin Tabbatar Da Tsaro A Kano
  • Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutane 2 A Kano – FRSC

Idan mun duba irin wadannan matakai da Amurka ta dauka a baya, da wadanda take dauka a yanzu, ma iya cewa a wannan karo gwamnatin Amurka mai ci ta rungumi manufofi da tsare-tsare mafiya haifar da rashin tabbas sama da na kowane lokaci a baya, ta yadda lamarin ya zamo babban kalubale ga yanayin kasuwancin duniya.

Wani abun lura ma shi ne yadda gwamnatin Amurka take ta kokarin dorawa kasar Sin laifinta na gazawa, da koma bayan da take fuskanta ta fannin bunkasar tattalin arziki, zarge-zargen da ko shakka ba su da wata makama.

A daya hannun kuma, duk da cewa karin harajin na gwamnatin Amurka mai ci na iya rage gibin cinikayya tsakaninta da Sin, amma kuma hakan zai haifar da karuwar gibin cinikayya tsakanin Amurka da wasu karin kasashen duniya, wanda hakan zai sabbaba koma baya ga tattalin arzikin duniya baki daya.

Labarai Masu Nasaba

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Masu fashin baki da dama na da ra’ayin cewa, tabbas illar wannan mataki na Amurka zai koma kanta, inda wasu daga sassan raya tattalin arzikin kasar kamar na albarkatun gona, da makamashi za su iya fuskantar matsin lamba mai tsanani. Yayin da wasu sassan kamfanonin kasar kuma ka iya fuskantar raguwar ribar da suke samu da kaso mai yawa, sakamakon karin kudaden hajojin da ake samarwa a masana’antun kasashen da Amurkan ta karawa haraji.

La’akari da wadannan illoli, kamata ya yi Amurka ta yi karatun ta nutsu, ta dakatar da matakan kakaba haraji marasa ma’ana, kana ta koma teburin tattaunawa, domin warware duk wani sabani na kasuwanci da cinikayya tare da dukkanin sassan da batun ya shafa, ta yadda za a gudu tare a tsira tare. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hainan: An Bude Dandalin Boao Na Asiya Na Bana 

Next Post

Ina Fatan Ci Gaba Da Kasancewa A Manchester United – Onana

Related

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

6 minutes ago
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya
Daga Birnin Sin

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

18 hours ago
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

19 hours ago
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 
Daga Birnin Sin

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

19 hours ago
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya
Daga Birnin Sin

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

21 hours ago
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

22 hours ago
Next Post
Ina Fatan Ci Gaba Da Kasancewa A Manchester United – Onana

Ina Fatan Ci Gaba Da Kasancewa A Manchester United - Onana

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

June 4, 2025
DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.