ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arzikin Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Amurka

A halin da ake ciki yanzu haka, yanayin tattalin arzikin duniya na fuskantar guguwar rashin tabbas, a gabar da Amurka ke kara tsaurara matakan kakaba haraji kan hajojin da ake shigarwa kasar daga wasu kasashen duniya, matakan da masana tattalin arziki daga sassan kasa da kasa ke ta suka, tare da bayyana su a matsayin illa da ka iya dakile ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya, baya ga ingiza hauhawar farashi, da gurgunta tsarin cinikayyar kasa da kasa da hakan zai haifar. 

Bisa halin da ake ciki, masu masana tattalin arziki na ganin matakan nan na kakaba karin haraji da Amurka ke aiwatarwa, za su ci gaba da zama barazana ga daidaiton tattalin arzikin duniya, kuma ko da kaso kadan daga cikin su Amurka ta aiwatar, hakan na iya tauye hasashen da aka yi na ci gaban tattalin arzikin duniya, tare da haifar da hauhawar farashi a Amurka ita kanta.

  • Sallah: ’Yansanda Sun Yi Alƙawarin Tabbatar Da Tsaro A Kano
  • Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutane 2 A Kano – FRSC

Idan mun duba irin wadannan matakai da Amurka ta dauka a baya, da wadanda take dauka a yanzu, ma iya cewa a wannan karo gwamnatin Amurka mai ci ta rungumi manufofi da tsare-tsare mafiya haifar da rashin tabbas sama da na kowane lokaci a baya, ta yadda lamarin ya zamo babban kalubale ga yanayin kasuwancin duniya.

ADVERTISEMENT

Wani abun lura ma shi ne yadda gwamnatin Amurka take ta kokarin dorawa kasar Sin laifinta na gazawa, da koma bayan da take fuskanta ta fannin bunkasar tattalin arziki, zarge-zargen da ko shakka ba su da wata makama.

A daya hannun kuma, duk da cewa karin harajin na gwamnatin Amurka mai ci na iya rage gibin cinikayya tsakaninta da Sin, amma kuma hakan zai haifar da karuwar gibin cinikayya tsakanin Amurka da wasu karin kasashen duniya, wanda hakan zai sabbaba koma baya ga tattalin arzikin duniya baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Fitar Da “Shirin Aiki Na Kasa Kan Hakkin Dan Adam Na (2026-2030)”  

Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya

Masu fashin baki da dama na da ra’ayin cewa, tabbas illar wannan mataki na Amurka zai koma kanta, inda wasu daga sassan raya tattalin arzikin kasar kamar na albarkatun gona, da makamashi za su iya fuskantar matsin lamba mai tsanani. Yayin da wasu sassan kamfanonin kasar kuma ka iya fuskantar raguwar ribar da suke samu da kaso mai yawa, sakamakon karin kudaden hajojin da ake samarwa a masana’antun kasashen da Amurkan ta karawa haraji.

La’akari da wadannan illoli, kamata ya yi Amurka ta yi karatun ta nutsu, ta dakatar da matakan kakaba haraji marasa ma’ana, kana ta koma teburin tattaunawa, domin warware duk wani sabani na kasuwanci da cinikayya tare da dukkanin sassan da batun ya shafa, ta yadda za a gudu tare a tsira tare. (Saminu Alhassan)

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da “Shirin Aiki Na Kasa Kan Hakkin Dan Adam Na (2026-2030)”  
  • Sulaiman
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
  • Sulaiman
    Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama

MASU ALAKA

Sin Ta Fitar Da “Shirin Aiki Na Kasa Kan Hakkin Dan Adam Na (2026-2030)”  
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da “Shirin Aiki Na Kasa Kan Hakkin Dan Adam Na (2026-2030)”  

June 11, 2026
Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
Daga Birnin Sin

Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya

June 11, 2026
Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar
Daga Birnin Sin

Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar

June 11, 2026
Next Post
Ina Fatan Ci Gaba Da Kasancewa A Manchester United – Onana

Ina Fatan Ci Gaba Da Kasancewa A Manchester United - Onana

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Fitar Da “Shirin Aiki Na Kasa Kan Hakkin Dan Adam Na (2026-2030)”  

Sin Ta Fitar Da “Shirin Aiki Na Kasa Kan Hakkin Dan Adam Na (2026-2030)”  

June 11, 2026
Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya

Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya

June 11, 2026
Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya

Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya

June 11, 2026
Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar

Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar

June 11, 2026
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Matsalar Tsaro: Manoma Sun Koma Gonakinsu A Katsina – Dikko Radda

June 11, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama

Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama

June 11, 2026
Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

June 11, 2026
An Rufe Makarantu A Mexico Saboda Fara Gasar Kofin Duniya

An Rufe Makarantu A Mexico Saboda Fara Gasar Kofin Duniya

June 11, 2026
An Kaddamar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Dan Adam Na Shekarar 2026 A Beijing

An Kaddamar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Dan Adam Na Shekarar 2026 A Beijing

June 11, 2026
Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

June 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.