• English
  • Business News
Tuesday, July 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jigawa Za Ta Zama Cibiyar Binciken Lafiya Nan Ba Da Jimawa Ba – Gwamna Namadi

by Bello Hamza
3 months ago
in Labarai
0
Jigawa Za Ta Zama Cibiyar Binciken Lafiya Nan Ba Da Jimawa Ba – Gwamna Namadi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Jigawa na ɗaukar matakai domin mayar da jihar cibiyar binciken lafiya, yayin da Gwamna Malam Umar Namadi ya ƙaddamar da ginin manyan cibiyoyin lafiya guda uku a Dutse, babban birnin jihar.

Cibiyoyin da aka fara gina su sun haɗa da Cibiyar Gwaje-gwaje ta zamani (Diagnostic Centre), Cibiyar Kula da Ciwon Zuciya (Cardiac Centre), da kuma Ginin Samar da Iskar Oxygen (Cryo-Oxygen Plant), waɗanda ake sa ran za su inganta harkar lafiya da kuma bunƙasa tattalin arziƙin jihar ta hanyar binciken lafiya.

  • Ina Da Ƙwarewar Da Zan Iya Zama Shugaban Ƙasar Nijeriya – Makinde
  • Gwamnati Ta Ayyana 18 Da 21 Ga Afrilu A Matsayin Hutun Esta

“Wannan ƙaddamarwar wani babban mataki ne a tafiyarmu na gina Jigawa,” in ji Gwamna Namadi.

“Mun riga mun fara inganta lafiya ta hanyar inshorar lafiya ga marasa ƙarfi da suka haura 143,000 da kuma gina sabbin cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko da na biyu.”

Ya bayyana cewa ko da yake gwamnati ce za ta ɗauki nauyin gina cibiyoyin, daga baya za a miƙa su ga kamfanonin zuba jari na lafiya ta hanyar tsarin haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da masu zaman kansu domin tabbatar da ɗorewarsu.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Zai Tarbi Gawar Buhari A Daura Don Yi Mata Jana’iza

Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima

“Waɗannan cibiyoyi ba iya Jigawa za su yi wa amfani ba, har ma da maƙwabta.

“Tare da sabbin na’urorin gwaje-gwaje irin su MRI da mammography, ba sai an je wasu jihohi domin samun irin waɗannan ayyuka ba,” in ji shi.

Gwamnan ya jaddada ƙudirinsa na ci gaba da inganta harkar kiwon lafiya a jihar, ta hanyar samar da sabbin ayyuka daidai da zamani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AikiCibiyoyiGwamna NamadiJigawaKiwon Lafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ina Da Ƙwarewar Da Zan Iya Zama Shugaban Ƙasar Nijeriya – Makinde

Next Post

Gwamnonin Nijeriya Sun Nuna Damuwarsu Kan Kashe-kashen Mutane A Filato 

Related

Tinubu Zai Tarbi Gawar Buhari A Daura Don Yi Mata Jana’iza
Manyan Labarai

Tinubu Zai Tarbi Gawar Buhari A Daura Don Yi Mata Jana’iza

2 hours ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima

3 hours ago
Sojoji Sun Daƙile Satar Mai, Sun Kama Mutane 50 A Neja Delta
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Satar Mai, Sun Kama Mutane 50 A Neja Delta

4 hours ago
Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

13 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari
Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

15 hours ago
Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami
Labarai

Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

15 hours ago
Next Post
Gwamnonin Nijeriya Sun Nuna Damuwarsu Kan Kashe-kashen Mutane A Filato 

Gwamnonin Nijeriya Sun Nuna Damuwarsu Kan Kashe-kashen Mutane A Filato 

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine

Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine

July 15, 2025
Tinubu Zai Tarbi Gawar Buhari A Daura Don Yi Mata Jana’iza

Tinubu Zai Tarbi Gawar Buhari A Daura Don Yi Mata Jana’iza

July 15, 2025
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima

Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima

July 15, 2025
Sojoji Sun Daƙile Satar Mai, Sun Kama Mutane 50 A Neja Delta

Sojoji Sun Daƙile Satar Mai, Sun Kama Mutane 50 A Neja Delta

July 15, 2025
Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

July 14, 2025
Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

July 14, 2025
Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

July 14, 2025
Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

July 14, 2025
Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

July 14, 2025
Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.