• English
  • Business News
Tuesday, September 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Jituwa Tsakanin Amurka Da China Na Iya Jefa Tattalin Arziƙin Duniya Cikin Hatsari – IMF

by Sadiq
4 months ago
in Manyan Labarai
0
Rashin Jituwa Tsakanin Amurka Da China Na Iya Jefa Tattalin Arziƙin Duniya Cikin Hatsari – IMF
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asusun bayar da lamuni na duniya (IMF), ya bayyana damuwa kan yadda rikicin kasuwanci tsakanin Amurka da China ke barazana ga ci gaban tattalin arziƙin duniya. 

A wani rahoto da aka fitar ranar Talata, IMF ta ce waɗannan ƙasashe biyu da ke riƙe da madafun iko a harkokin tattalin arziƙin duniya suna haddasa matsaloli da ka iya jefa duniya cikin koma baya.

  • Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Siyasantar Da Batun Asalin Cutar COVID-19 
  • An Kimtsa Tsaf Don Kaddamar Da Aikin Binciken Kumbon Shenzhou-20 Na Kasar Sin 

Rahoton ya bayyana cewa harajin da Amurka ke ƙaƙaba wa China da wasu ƙasashe na hana walwalar cinikayya da ke da muhimmanci ga ci gaban duniya.

Kamar yadda rahoton ya nuna, IMF ta rage hasashen yadda tattalin arziƙin duniya zai tafi a shekarar 2025, inda ta ce maimakon a samu kashi 3 na ci gaba, za a samu kashi 2.8 ko ƙasa da haka.

Har ila yau, ana ganin cewa a shekarar 2026 tattalin arziƙin duniya zai shiga wani mawuyacin hali fiye da yadda aka zata.

Labarai Masu Nasaba

2027: Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Daba 107 A Kano, Sun Ƙwato Makamai Da Ƙwayoyi

Shugaban sashen tsare-tsare na IMF, Pierre-Olivier Gourinchas, ya shaida wa manema labarai cewa duniya na shiga wani sabon lokaci na ruɗani a fannin tattalin arziƙi, wanda zai iya rushe tsarin da aka shafe kusan shekaru 80 ana ginawa.

Ya ƙara da cewa harajin da ƙasashe ke ƙaƙaba wa juna da kuma rashin tabbas a manufofin kasuwanci suna daga cikin manyan dalilan da ke kawo wannan koma baya.

Rahoton na IMF na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan gwamnatin Amurka ta ƙara wasu sabbin haraji kan kayayyakin da ke shiga da su ƙasar daga waje, lamarin da ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin masana da ƙasashe masu ruwa da tsaki.

IMF ta shawarci ƙasashen duniya da su zauna a teburin sulhu domin kawo ƙarshen rashin jituwa da ke hana ci gaban tattalin arziƙi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaChinaGargaɗiHarajiIMFKoma bayaTattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sabbin Haraji: Yadda ‘Yan Bindiga Ke Tilasta Wa Jama’a Biyan Miliyoyin Kuɗi A Zamfara

Next Post

Ba ‘Yan Nijeriya Ne Ke Kai Mana Hare-hare A Benuwai Ba – Gwamna Alia

Related

Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike
Manyan Labarai

2027: Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi

8 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Daba 107 A Kano, Sun Ƙwato Makamai Da Ƙwayoyi

9 hours ago
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Ƙarin Kasafin Naira Biliyan 215.3 A Na 2025

19 hours ago
Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

23 hours ago
Gwamnan Neja Ya Kori Kwamishinoninsa Gaba Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnan Neja Ya Kori Kwamishinoninsa Gaba Ɗaya

1 day ago
Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara – El-Rufai
Manyan Labarai

Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara – El-Rufai

1 day ago
Next Post
Ba ‘Yan Nijeriya Ne Ke Kai Mana Hare-hare A Benuwai Ba – Gwamna Alia

Ba 'Yan Nijeriya Ne Ke Kai Mana Hare-hare A Benuwai Ba - Gwamna Alia

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

September 2, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Masu Safarar Makamai A Katsina, Sun Ƙwato Makamai

September 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Sace Adaidaita Sahu A Borno

September 2, 2025
Zargin Cin Hanci: Babu Wani Shirin Tsige El-Rufai – Kakakin Majalisar Dokokin Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Gargaɗi El-Rufai Kan Yunƙurin Tayar Da Rikici A Jihar

September 2, 2025
Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike

2027: Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi

September 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Daba 107 A Kano, Sun Ƙwato Makamai Da Ƙwayoyi

September 2, 2025
Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

September 1, 2025
Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

September 1, 2025
Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

September 1, 2025
AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

September 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.