Wakilin musamman na shugaban kasar Sin Xi Jinping, Mu Hong, zai halarci bikin rantsar da shugaban kasar Gabon, Brice Clotaire Oligui Nguema, a Libreville, babban birnin kasar, a ranar 3 ga watan Mayu, bisa gayyatar da shugaba Nguema ya yi masa.
Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar a ranar Larabar da ta gabata.
Mu shi ne mataimakin shugaban kwamitin majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp