• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hutun Ranar Ma’aikata Na Kasar Sin Ya Haskawa Duniya Karfin Tattalin Arzikin Kasar

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Sin

Hukumomi a kasar Sin sun yi kiyasin an yi tafiye-tafiye miliyan 314 yayin hutun ma’aikata da aka yi tsakanin ranar 1 zuwa 5 ga watan Mayu, adadin da ya karu kan na bara da kaso 6.4. Kana adadin kudin da aka kashe wajen yawon bude ido shi ma ya karu, wanda ya kai yuan biliyan 180.3, kwatankwacin dala biliyan 25, karuwar kaso 8 kan na bara. 

Mai karatu, shin me hakan ke nufi?

Tabbas a duk inda muka ji karuwar tafiye-tafiye ko kashe kudi tsakanin al’umma, to alama ce ta karfin tattalin arzikin kasa da ma arzikin dake hannun ’yan kasa. Zan iya cewa abun dariya ne idan kasar Sin ta ayyana burin ci gaban tattalin arzikinta na shekara, sannan na ji kafafen yada labarai na kasashen yamma na nuna shakku kan yadda za ta cimma burinta. A iya tsawon zamana a kasar Sin, ban taba jin ta furta wani burin da ta gaza cimmawa ba. Har kullum walwalar al’ummarta da ci gabansu, shi ne babban burin da kasar ta sanya a gaba, kuma a zahiri ake ganin hakan.

Abu na biyu shi ne, kudin da aka kashe a bangaren yawon bude ido shi ma ya karu kan na bara da kaso 8, lamarin dake nuna yadda kasar Sin ke mayar da hankali ga bangaren bude ido musamman wanda ya shafi raya al’adu. Duk wanda ya san kasar Sin, to ya san cewa kasa ce mai matukar mayar da hankali kan rayawa da yayata al’adunta, domin ita ba ta taba sakin al’adunta ta kama na wani ba.

Akwai kuma batun ci gaba da kayayyakin more rayuwa. Hakika tafiye-tafiye ba za su yiwu ba idan babu kyawawan tituna ko layukan dogo ko kyakkyawan tsare tsaren sufuri kamar na jiragen sama da na ruwa da sauransu. Yawaitar tafiye tafiye da aka gani tsakanin al’ummar Sinawa, ya kara haskawa duniya ci gaban kasar Sin da ingantattun ababen more rayuwa dake akwai a kasar.

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Sai kuma uwa uba zaman lafiya. Sai da zaman lafiya za a samu kwanciyar hankali har ma a kashe kudi ko a je yawon bude ido da sauran harkoki. Wannan hutu ya kara bayyana cewa, al’ummar kasar Sin suna more zaman lafiya, kuma mabanbantan kabilu a kasar na zaman jituwa da juna.

Hakika kasar Sin ta yi gaba, kuma dogaro da ta yi da karfinta da ma tsara manufofin da suka dace da ita, su ne ginshinkin ci gabanta, wanda babu wani daga waje da zai iya rusawa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik
Daga Birnin Sin

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
Daga Birnin Sin

Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 2, 2025
Next Post
Kashi Na Biyu Na Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Sin Ta Tashi Zuwa Abyei

Kashi Na Biyu Na Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Sin Ta Tashi Zuwa Abyei

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

November 3, 2025
Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

November 3, 2025
Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

November 3, 2025
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

November 3, 2025
Likitoci

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

November 3, 2025
Kano

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.