ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hutun Ranar Ma’aikata Na Kasar Sin Ya Haskawa Duniya Karfin Tattalin Arzikin Kasar

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Sin

Hukumomi a kasar Sin sun yi kiyasin an yi tafiye-tafiye miliyan 314 yayin hutun ma’aikata da aka yi tsakanin ranar 1 zuwa 5 ga watan Mayu, adadin da ya karu kan na bara da kaso 6.4. Kana adadin kudin da aka kashe wajen yawon bude ido shi ma ya karu, wanda ya kai yuan biliyan 180.3, kwatankwacin dala biliyan 25, karuwar kaso 8 kan na bara. 

Mai karatu, shin me hakan ke nufi?

Tabbas a duk inda muka ji karuwar tafiye-tafiye ko kashe kudi tsakanin al’umma, to alama ce ta karfin tattalin arzikin kasa da ma arzikin dake hannun ’yan kasa. Zan iya cewa abun dariya ne idan kasar Sin ta ayyana burin ci gaban tattalin arzikinta na shekara, sannan na ji kafafen yada labarai na kasashen yamma na nuna shakku kan yadda za ta cimma burinta. A iya tsawon zamana a kasar Sin, ban taba jin ta furta wani burin da ta gaza cimmawa ba. Har kullum walwalar al’ummarta da ci gabansu, shi ne babban burin da kasar ta sanya a gaba, kuma a zahiri ake ganin hakan.

ADVERTISEMENT

Abu na biyu shi ne, kudin da aka kashe a bangaren yawon bude ido shi ma ya karu kan na bara da kaso 8, lamarin dake nuna yadda kasar Sin ke mayar da hankali ga bangaren bude ido musamman wanda ya shafi raya al’adu. Duk wanda ya san kasar Sin, to ya san cewa kasa ce mai matukar mayar da hankali kan rayawa da yayata al’adunta, domin ita ba ta taba sakin al’adunta ta kama na wani ba.

Akwai kuma batun ci gaba da kayayyakin more rayuwa. Hakika tafiye-tafiye ba za su yiwu ba idan babu kyawawan tituna ko layukan dogo ko kyakkyawan tsare tsaren sufuri kamar na jiragen sama da na ruwa da sauransu. Yawaitar tafiye tafiye da aka gani tsakanin al’ummar Sinawa, ya kara haskawa duniya ci gaban kasar Sin da ingantattun ababen more rayuwa dake akwai a kasar.

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Sai kuma uwa uba zaman lafiya. Sai da zaman lafiya za a samu kwanciyar hankali har ma a kashe kudi ko a je yawon bude ido da sauran harkoki. Wannan hutu ya kara bayyana cewa, al’ummar kasar Sin suna more zaman lafiya, kuma mabanbantan kabilu a kasar na zaman jituwa da juna.

Hakika kasar Sin ta yi gaba, kuma dogaro da ta yi da karfinta da ma tsara manufofin da suka dace da ita, su ne ginshinkin ci gabanta, wanda babu wani daga waje da zai iya rusawa.

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

MASU ALAKA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
Daga Birnin Sin

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Next Post
Kashi Na Biyu Na Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Sin Ta Tashi Zuwa Abyei

Kashi Na Biyu Na Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Sin Ta Tashi Zuwa Abyei

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.