• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

by Abubakar Abba
3 weeks ago
in Noma Da Kiwo
0
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akasarin masu kiwaon Kifi, na dogara ne a kan kasancenwar yadda yanayi yake, musamman na samar da tsaftataccen ruwa da kuma yadda yanayi zai kasance na zafi ko sanyi, wanda hakan musamman zai ba su damar sanin samun sauyin yanayi.

Babban abin da ke shafar masu sana’ar  kiwon Kifi shi ne, samun yanayin zafi ko na sanyi da kuma samun sauyi na saukar ruwan sama, wanda ke jawo afkuwar annobar ambaliyar ruwan sama da fari.

Wata illar kuma na afkwa ne a cikin dan kankanin lokaci, misali samun ruwan sama kamar da bakin kwarya, inda kuma wata illar ke afkuwa ta dogon zango, wanda za a rika samun sauyi a hankali a hankali.

  • Sabbin Fasahohin Noma Na Zamani Na Ci Gaba Da Bayyana A Kasar Sin
  • Boko Haram Sun Kashe Masu Kamun Kifi 18 A Borno

1- Wanzar Da Dabarun  Kula Da Kiwon Kifin Yadda Ya Dace:

 A cewar Soto, “Wanzar da dabarun kula da kiwon kifi ne mataki na farko na jure wa sauyin yanayi ne zai inganta wajen kiwon su tare da ba su kariya daga kamuwa da cututtuka, sakamakon sauyin yanayi, duba da yadda garkuwar jikin dabbobi ta take, domin kuwa ba sa son yanayi na takura”.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

Duba da yadda yanayin muhalli yake, zai  ba da dama wajen rage fuskantar sauyin yanayi tare da inganta kiwon lafiyarsu, abincinsu da kuma ingancin ruwan shansu.

2- Fashin Baki Kan Abin Da Zai Iya Afkuwa A Wajen Kiwon Su:

Ga wanda zai fara wannan kiwo, ana so ya zabi wajen da ya dace da kuma tsarin da zai yi, don guje wa abin da zai iya afkuwa a bangaren sauyin yanayi mai tsanani.

3- Raba Kafa A Yayin Kiwon: Masu iya magana na cewa, ‘Ba a zuba kwai a cikin kwando daya’, wato ma’ana, ana so ka raba kafa ta hanyar yin wata dabara a kan kayanka, don kaucewa yin asara.

Kazalika, raba kafa na taimakawa wajen kara bunkasa kiwo da kuma kara sama wa mai kiwon kudin shiga.

4- Amfani Da Gargadin Farko: Ana so masu kiwo su rika bibiyar bayanai a kan afkuwar sauyin yanayi, wanda hakan zai ba su damar daukar mataki a kan lokaci, domin su kauce wa yin asara.

5- Amfani Da Ingannatun Kayan Aiki Don Yin Kiwo:

Kwamin kiwonsu da ake ginawa a kasa da kuma wanda ake ginawa a kan tudu, ana so a ba su kariya daga afkuwar ambaliyar ruwa. Kazalika, ana so kwamin ya kasance mai zurfi, domin bayar da kariya daga fari da kuma yanayi mai zafi.

6 Ana So Mai Wannan Kiwo Ya Rika Tuntubar Sauran Masu Kiwo:

Akasarin masu kiwo, ba zai yiwu su tafiyar da komai su kadai ba, saboda haka, ana bukatar su rika tuntubar sauran kungiyoyin da ke kiwon Kifi; don samun shawarwarin da za su taimaka musu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FishFish farmingKifiNoman Kifi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

Next Post

Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

Related

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 day ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 day ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 day ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

1 week ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

1 week ago
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

2 weeks ago
Next Post
Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

June 1, 2025
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

June 1, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

June 1, 2025
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

June 1, 2025
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

June 1, 2025
Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

June 1, 2025
Yadda Za Ki Hada Funkasonki

Yadda Za Ki Hada Funkasonki

June 1, 2025
Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.