ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

by Abubakar Abba and Sulaiman
11 months ago
Kifi

Gwamnatin Tarayya ta kuduri aniyar dakatar da shigo da Kifi daga kasashen ketare, wanda aka jima ana yi fitonsa.

A cewar gwamnatin tarayyar, za ta kawo karshin hakan ne ta hanyar bunkasa kamun Kifin a cikin gida Nijeriya.

  • Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa
  • An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa

Kazalika, za ta yi hakan ne, musamman domin kara karfafa samar da wadataccen abinci a kasar da samar da ayyukan yi da kuma kara karfafa fitar da kayan da ba su shafi fannin mai ba.

ADVERTISEMENT

Ministan Bunkasa Tattalin Arzikin Teku, Adegboyega Oyetola ne ya sanar da hakan, a yayin wata ganawa da shugabanin kungiyoyin masu kamun Kifi a Abuja.

Ma’aikatar Ministan ce ta shirya ganawar, kan kokarin da gwamnatin tarayya ke ci gaba da yi, na saita fannin kamun Kifin a kasar.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

“Dole ne kasar nan ta samar da wata sabuwar hanya, domin samar da Kifin da zai wadace ta, wanda hakan zai kuma taimaka matuka wajen rage dogaro da shigo da Kifin daga kasashen waje da kuma kara habaka fannin” in ji Ministan.

Oyetola ya kara da cewa, gwamnatin tarayya ta himmatu kwarai da gaske wajen bai wa fannin goyon bayan da ya dace, musamman ta hanyar yin amfani da tsarin kimiyyar fasahar zamani da kuma zuba makudan kudade a fannin.

Kazalika, ya jaddada cewa; gwamnatin tarayya za ta kara kaimi wajen ganin ana samar da wadataccen Kifi a kasar, musamman domin rage dogaro a kan wadanda ake shigowa da su daga kasashen ketare, duba da cewa; fannin na bayar da gagarumar gudunmawa wajen kara bunkasa tattalin azikin kasar.

Kungiyoyiyon da suka halarci ganawar sun hada; manya-manyan masu ruwa da tsaki a fannin na kamun Kifi, kungiyar masu kamun Kifi ta kasa (FCFN), kungiyar masu kama dabbobin ruwa (TADAN), kungiyar masu kiwon Tarwada ta kasa (CAFAN) da sauran makamantansu.

Babban mai bai wa ministan shawara a fanin yada labarai, Bolaji Akinola, a cikin sanwar da ya bayar; bayan kammala taron ya bayyana cewa; Oyetola ya shaida wa mahalartan cewa, ma’aikatar na kara yin kokari wajen tallafa wa mata da matasa da suka rungumi sana’ar yin kiwon Kifi a karkashin shirye-shiyen da ma’aikatar ta kirkiro.

A cewar ministan, wannan shiri ne na tallafa wa mata da matasa; wanda kuma ya hada da tallafa musu da rance da kayan aiki, musaman don kara musu kwarin gwiwa, domin bayar da tasu gudunmawar wajen kara bunkasa fannin a Nijeriya, wanda kuma ya yi daidai na shirin Shugaban Kasa Bola Tinubu (Renewed Hope Agenda).

“Kara yawan matasan da za su rungumi sana’ar kiwon Kifi, wani babban maki ne, na kara samar da wadataccen abinci a fadin wannan kasa, wanda hakan zai kuma kasance wani mataki ne na rage marasa yin aiki a kasar” a cewar Oyetola.

“Mun mayar da hankali wajen tabatar da cewa, ba a bar mata da matasan kasar nan a baya ba, musamman don ganin an inganta rayuwarsu”, in ji Ministan.

A wajen ganawar, masu ruwa da tsaki a fannnin; sun kuma bijiro da wasu kalubale da ke ci gaba da ci wa fannin tuwo a kwarya.

A cewarsu, kalubalen sun hada da; yawan kamun Kifayen a Kogi, rashin samun rance, karancin kayan adana Kifin da ake adana Kifin bayan kamo su.

Sauran su ne, tsadar abincin da ake ciyar da su, wadanda ake shigo wa da su daga ketare, matsalar safararsu, karbar haraji barkatai, wanda ke sanyawa matasa ba sa iya shiga cikin sana’ar.

Sai dai, Oyetola ya bai wa masu ruwa da tsakin tabbacin cewa, wadannan kalubale da suka bijro da su, ma’aikatar za ta lalubo da mafita a kansu.

A cewarsa,  a yanzu ana kan tattaunawa da Bankin Duniya, musamman domin a samu rancen kudi don tallafa wa masu kiwon Kifin a kasa tare da kuma samar musu da Inshora.

Ministan ya ci gaba da cewa, wannan zai kara tabbatar da nasarar da aka samu a shirin zamani na kamun dabbobin ruwa a Dam din Oyan da kuma sauran yankunan da ma’aikatar tasa ta yi hadaka da ma’aikatar albarkatun ruwa ta tarayya da sauran hukumomin gwamnatin tarayya.

“Wannan ganawa, ba iya nan za ta tsaya ba; amma tamkar yanzu ne aka fara ta, domin za a ci gaba da tattaunawa kan yadda za a ci gaba da habaka fannin,” in ji shi.

Shi kuwa a nasa jawabin, Wellington Omoragbon, Daraktan kula da kamun Kifi da sauran dabbobin ruwa, ya sanar da muhimmancin bukatar kara karfafa hadaka, domin jawo masu son zuba hannun jari a fannin, musamman domin a kara samar da wadataccen Kifi a fadin kasar baki-daya.

Kifi
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
Kifi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.