ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

by Abubakar Abba
1 year ago
Noma

A makwannin da suka gabata, yankuna da dama na kasar nan, sun samu ruwan sama kamar da bakin kwarya. Hukumar kula da yanayi ta kasa (NiMet), a ranar 4 ga watan Fabrairun 2025, ta kaddamar da kundin hasashe kan yadda yanayi zai kasance a kakar noman shekarar 2025.

Kundin ya yi hasashen cewa, za a samu ruwan sama kamar da bakin kwarya a wannan shekara da muke ciki (bana), wanda ruwan saman, mai yiwuwa zai sauka da wuri a shekarar 2025 din.

Tuni dai, kamar yadda dai aka saba, wasu manoma a kasar duk da cewa, daminar kakar 2025 din ba ta riga ta kankama ba, suka fara yin shuka a gonakinsu.

ADVERTISEMENT
  • Radda Ya Raba Wa Manoma Taki A Jihar Katsina
  • Sabbin Fasahohin Noma Na Zamani Na Ci Gaba Da Bayyana A Kasar Sin

Misali, rahotannin sun bayyana cewa, a Kananan Hukumomin Akwanga, Lafia da Doma da ke Jihar Nasarawa, sun shuka Irin gyada kawai domin sa ran samun ruwan sama a makon da ya gabata, wanda hakan ya sanya yanzu suke jin tsoro ganin cewa, ba a sake yin wani ruwan saman ba, hakan ya kuma sanya Irin gyadar da suka shuka, zafin rana ya fara lalata shi.

Haka nan ma, batun yake a babban birnin tarayyar Abuja, kamar yadda wasu rahotanni suka bayyana, musamman ga wasu  manoman da ke zaune a wasu sassa na Bwari da kuma wasu kauyuka da ke makwabtaka da Jihar Neja, da suka yi hanzarin yin shuka, su ma suka shiga cikin fargaba ta rashin samun sake saukar ruwan na sama.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Bugu da kari, wasu kwararru a fannin aikin noma, su ma tuni suka gargadi manoman kan kaucewa yin shuka da wuri, inda suka shawarce su da su tabbatar da sun kiyaye da hasashen na hukumar ta NiMet, domin kaucewa tabka asara da kuma yin da-na-sani.

Lokacin Da Ya Fi Dacewa Manona Su Yi Shuka:

Wata kungiya mai bayar da agajin gaggawa, (Christian Aids) tare da hadaka da wasu abokan hudda, sun samar da wata taswira da ke kunshe da lokacin da ya fi dacewa manoman da ke jihohin kasar 36 ciki har da babban birnin tarayayyar Abuja, su yi shuka.

Taswirar wadda ta kasance mai saukin amfanai, sun tsara matakan da suka kamata manoman su bi, na kiyaye lokacin yin shuka, mussamman domin manoman su kauce wa fadawa cikin matsalar irin yadda suka tsinci kansu a ciki a kakar noman shekarar 2024.

Idan za a iya tunawa, hukumar ta NiMet, a wasu bayanai da ta wallafa na farko da suka kuma karade shafukan sada zumunta na zamani a 2025, ta sanar da manoman kasar, ranakun da ya kamata su fara yin shuka da kuma Irin da ya kamata su shuka.

Kazalika, hukumar ta kuma shawarci manoman da su gujewa yin shuka da wuri, duba da bayanan sauyin yanayi da hukumar ta yi hasashen za a iya samu a kasar.

Idan za a iya tunawa, a kakar noma ta shekarar 2024, wasu manoman kasar da dama da suka yi shuka da wuri, sun tabka mummunar asara.

Wani malamain gona mai suna Jacob Auta, ya shawarci manoman kasar cewa; kada su yi saurin yin shuka, inda ya kara da cewa; duba da yadda Irin noma ya yi tsada, ya zama wajibi manoman su sanya ido kafin su fara yin shuka.

Ya yi nuni da cewa, wasu daga cikin Irin noman, ba sa iya jurewa yanayi kamar na zafi, idan an shuka su.

Jacob ya kara da cewa, idan har manoman sun yi shuka kuma ya kasance an kai sama da mako daya ba a samu ruwan sama ba, za su iya tafka asara.

“Haka nan, batun yake a kan sauran amfanin gona, sai dai kawai idan manomi, yana da kayan ban ruwan da zai iya rika yi wa gonarsa ban ruwa,”  in ji Jacob.

Noma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.