ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

by Abubakar Abba
1 year ago
Noma

A makwannin da suka gabata, yankuna da dama na kasar nan, sun samu ruwan sama kamar da bakin kwarya. Hukumar kula da yanayi ta kasa (NiMet), a ranar 4 ga watan Fabrairun 2025, ta kaddamar da kundin hasashe kan yadda yanayi zai kasance a kakar noman shekarar 2025.

Kundin ya yi hasashen cewa, za a samu ruwan sama kamar da bakin kwarya a wannan shekara da muke ciki (bana), wanda ruwan saman, mai yiwuwa zai sauka da wuri a shekarar 2025 din.

Tuni dai, kamar yadda dai aka saba, wasu manoma a kasar duk da cewa, daminar kakar 2025 din ba ta riga ta kankama ba, suka fara yin shuka a gonakinsu.

ADVERTISEMENT
  • Radda Ya Raba Wa Manoma Taki A Jihar Katsina
  • Sabbin Fasahohin Noma Na Zamani Na Ci Gaba Da Bayyana A Kasar Sin

Misali, rahotannin sun bayyana cewa, a Kananan Hukumomin Akwanga, Lafia da Doma da ke Jihar Nasarawa, sun shuka Irin gyada kawai domin sa ran samun ruwan sama a makon da ya gabata, wanda hakan ya sanya yanzu suke jin tsoro ganin cewa, ba a sake yin wani ruwan saman ba, hakan ya kuma sanya Irin gyadar da suka shuka, zafin rana ya fara lalata shi.

Haka nan ma, batun yake a babban birnin tarayyar Abuja, kamar yadda wasu rahotanni suka bayyana, musamman ga wasu  manoman da ke zaune a wasu sassa na Bwari da kuma wasu kauyuka da ke makwabtaka da Jihar Neja, da suka yi hanzarin yin shuka, su ma suka shiga cikin fargaba ta rashin samun sake saukar ruwan na sama.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Bugu da kari, wasu kwararru a fannin aikin noma, su ma tuni suka gargadi manoman kan kaucewa yin shuka da wuri, inda suka shawarce su da su tabbatar da sun kiyaye da hasashen na hukumar ta NiMet, domin kaucewa tabka asara da kuma yin da-na-sani.

Lokacin Da Ya Fi Dacewa Manona Su Yi Shuka:

Wata kungiya mai bayar da agajin gaggawa, (Christian Aids) tare da hadaka da wasu abokan hudda, sun samar da wata taswira da ke kunshe da lokacin da ya fi dacewa manoman da ke jihohin kasar 36 ciki har da babban birnin tarayayyar Abuja, su yi shuka.

Taswirar wadda ta kasance mai saukin amfanai, sun tsara matakan da suka kamata manoman su bi, na kiyaye lokacin yin shuka, mussamman domin manoman su kauce wa fadawa cikin matsalar irin yadda suka tsinci kansu a ciki a kakar noman shekarar 2024.

Idan za a iya tunawa, hukumar ta NiMet, a wasu bayanai da ta wallafa na farko da suka kuma karade shafukan sada zumunta na zamani a 2025, ta sanar da manoman kasar, ranakun da ya kamata su fara yin shuka da kuma Irin da ya kamata su shuka.

Kazalika, hukumar ta kuma shawarci manoman da su gujewa yin shuka da wuri, duba da bayanan sauyin yanayi da hukumar ta yi hasashen za a iya samu a kasar.

Idan za a iya tunawa, a kakar noma ta shekarar 2024, wasu manoman kasar da dama da suka yi shuka da wuri, sun tabka mummunar asara.

Wani malamain gona mai suna Jacob Auta, ya shawarci manoman kasar cewa; kada su yi saurin yin shuka, inda ya kara da cewa; duba da yadda Irin noma ya yi tsada, ya zama wajibi manoman su sanya ido kafin su fara yin shuka.

Ya yi nuni da cewa, wasu daga cikin Irin noman, ba sa iya jurewa yanayi kamar na zafi, idan an shuka su.

Jacob ya kara da cewa, idan har manoman sun yi shuka kuma ya kasance an kai sama da mako daya ba a samu ruwan sama ba, za su iya tafka asara.

“Haka nan, batun yake a kan sauran amfanin gona, sai dai kawai idan manomi, yana da kayan ban ruwan da zai iya rika yi wa gonarsa ban ruwa,”  in ji Jacob.

Noma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.