• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Afirka Da Sin Na Taimakawa Raya Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Hadin Gwiwar Afirka Da Sin Na Taimakawa Raya Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duniyarmu na fuskantar matsalolin da suka hada da yake-yake, da rashin tsaro, da koma bayan tattalin arziki, da karancin abinci, da annoba.

Wannan yanayi ya sa ake bukatar wani mataki da zai taimaka wajen saukaka yanayin da ake ciki da raya duniyarmu.

  • Sin: Hadin Gwiwar Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Haifar Da Sakamako Mai Kyau Da Fa’ida

To ko hadin gwiwar kasashen Afirka da kasar Sin, zai iya biyan bukatunmu a wannan fanni?
An gudanar da taron kolin masu tsara aiwatar da ayyukan da suka biyo bayan taron ministoci na 8, na dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC)  ta kafar bidiyo jiya, inda manyan jami’an bangarorin Afirka da Sin, suka gabatar da hadaddiyar sanarwa da jawabai, wadanda suka nuna yadda hadin gwiwar bangarorin 2 ke taimakawa raya duniyar mu, musamman ta fannoni 2 dake kasa:
Da farko, hadin kan Afirka da Sin, ya sa ana samun hakikanin ci gaba.

An gudanar da taron ministoci na 8 na dandalin FOCAC a kasar Senegal, fiye da watanni 8 da suka wuce. Sai dai yaya ake aiwatar da yarjeniyoyin da aka cimma wajen taron?

A taro na wannan karo, an yi bayani kan wasu nasarorin da aka samu: Cikin fiye da watanni 8 da suka wuce, kamfanonin kasar Sin sun kammala ayyukan gina wasu manyan kayayyakin more rayuwa a kasashen Afirka, da suka hada da babbar gadar Fanggioni ta kasar Senegal, da tagwayen hanyoyi dake dab da filin jiragen sama na kasar Kenya, da babbar hanyar mota ta Kribi-Lolabe dake kasar Kamaru, da dai sauransu. Kana cikin watanni 7 da wuka wuce, kasar Sin ta shigo da kayayyaki masu darajar dala biliyan 70.6 daga kasashen Afirka, da zuba dala biliyan 2.17 ga kasuwannin Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Ban da wannan kuma, an tanadi ayyukan da za a gudanar da su kamar haka: kasar Sin za ta yafe wa wasu kasashe 17 dake nahiyar Afirka bashin da take binsu, da samar da karin tallafin abinci ga wasu kasashen da suke da bukata, da kara jiragen sama masu daukar fasinjoji, da suke zirga-zirga tsakanin Afirka da Sin, da dai sauransu.

Duk wata yarjejeniyar da aka kulla a baya, za a aiwatar da ita. Sa’an nan a yi cikakken bayani kan shirin da za a gudanar, don tabbatar da cika alkawuran. Wannan ya nuna yadda ake hadin gwiwa tsakanin Afirka da Sin don neman hakikanin ci gaba.

Sa’an nan, fanni na biyu shi ne, hadin gwiwar Afirka da Sin, a bude yake ga sauran bangarori.

Shin ko kasar Sin tana yin hadin gwiwa da kasashen Afirka don neman shawo kansu, da samun moriyar siyasa? Batun ba haka yake ba. Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya bayyana a wajen taron jiya cewa, “ Kasar Sin na son ganin gamayyar kasa da kasa sun ci gaba da mai da hankali kan kasashen Afirka, da nuna musu goyon baya.

Idan kasashen Afirka sun yarda, za a iya yin hadin kai tsakanin bangarori 3 ko fiye, a nahiyar Afirka. Kasashen Afirka suna bukatar wani yanayi na kwanciyar hankali da sada zumunta, maimakon ra’ayin yakin cacar baka, kana suna maraba da hadin gwiwar da zai amfani jama’a, maimakon shiga takarar wasu manyan kasashe.” Wannan magana ta nuna yadda bangaren Sin ke fahimtar ra’ayin kasashen Afirka.

Ta hanyar yin bincike kan tarihin hadin gwiwar Sin da Afirka, za mu iya fahimtar cewa, kasashen Afirka da kasar Sin, sun yi watsi da tunani na yakin cacar baka, wanda har yanzu kasashen yamma suke tsayawa a kai.

Sa’an nan sun juya ga tunanin al’ummar dan Adam mai makomar bai daya. Wanne ne daga cikin su zai fi amfanar al’ummun duniya?

Na san kowa zai iya ba da amsa.
Magance sabanin ra’ayi, da neman cimma matsaya, da kokarin hadin gwiwa don daidaita matsalolin da ake fuskanta, da neman samun hakikanin ci gaba, wannan shi ne ra’ayin da zai iya taimakawa, wajen kyautata yanayin da duniyarmu ke ciki, kuma babbar manufa ce da kasashen Afirka da kasar Sin ke tsayawa a kai, yayin da suke hadin gwiwa da juna. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Matuka Jirgi Suka Shantake Da Bacci A Lokacin Sauka

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Lauya A Zamfara

Related

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

16 hours ago
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

17 hours ago
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko
Daga Birnin Sin

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

18 hours ago
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba
Daga Birnin Sin

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

19 hours ago
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
Daga Birnin Sin

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

20 hours ago
An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya
Daga Birnin Sin

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

21 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Lauya A Zamfara

'Yan Bindiga Sun Hallaka Lauya A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.