ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Afirka Da Sin Na Taimakawa Raya Duniya

by CMG Hausa
4 years ago
Afirka

Duniyarmu na fuskantar matsalolin da suka hada da yake-yake, da rashin tsaro, da koma bayan tattalin arziki, da karancin abinci, da annoba.

Wannan yanayi ya sa ake bukatar wani mataki da zai taimaka wajen saukaka yanayin da ake ciki da raya duniyarmu.

  • Sin: Hadin Gwiwar Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Haifar Da Sakamako Mai Kyau Da Fa’ida

To ko hadin gwiwar kasashen Afirka da kasar Sin, zai iya biyan bukatunmu a wannan fanni?
An gudanar da taron kolin masu tsara aiwatar da ayyukan da suka biyo bayan taron ministoci na 8, na dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC)  ta kafar bidiyo jiya, inda manyan jami’an bangarorin Afirka da Sin, suka gabatar da hadaddiyar sanarwa da jawabai, wadanda suka nuna yadda hadin gwiwar bangarorin 2 ke taimakawa raya duniyar mu, musamman ta fannoni 2 dake kasa:
Da farko, hadin kan Afirka da Sin, ya sa ana samun hakikanin ci gaba.

ADVERTISEMENT

An gudanar da taron ministoci na 8 na dandalin FOCAC a kasar Senegal, fiye da watanni 8 da suka wuce. Sai dai yaya ake aiwatar da yarjeniyoyin da aka cimma wajen taron?

A taro na wannan karo, an yi bayani kan wasu nasarorin da aka samu: Cikin fiye da watanni 8 da suka wuce, kamfanonin kasar Sin sun kammala ayyukan gina wasu manyan kayayyakin more rayuwa a kasashen Afirka, da suka hada da babbar gadar Fanggioni ta kasar Senegal, da tagwayen hanyoyi dake dab da filin jiragen sama na kasar Kenya, da babbar hanyar mota ta Kribi-Lolabe dake kasar Kamaru, da dai sauransu. Kana cikin watanni 7 da wuka wuce, kasar Sin ta shigo da kayayyaki masu darajar dala biliyan 70.6 daga kasashen Afirka, da zuba dala biliyan 2.17 ga kasuwannin Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Ban da wannan kuma, an tanadi ayyukan da za a gudanar da su kamar haka: kasar Sin za ta yafe wa wasu kasashe 17 dake nahiyar Afirka bashin da take binsu, da samar da karin tallafin abinci ga wasu kasashen da suke da bukata, da kara jiragen sama masu daukar fasinjoji, da suke zirga-zirga tsakanin Afirka da Sin, da dai sauransu.

Duk wata yarjejeniyar da aka kulla a baya, za a aiwatar da ita. Sa’an nan a yi cikakken bayani kan shirin da za a gudanar, don tabbatar da cika alkawuran. Wannan ya nuna yadda ake hadin gwiwa tsakanin Afirka da Sin don neman hakikanin ci gaba.

Sa’an nan, fanni na biyu shi ne, hadin gwiwar Afirka da Sin, a bude yake ga sauran bangarori.

Shin ko kasar Sin tana yin hadin gwiwa da kasashen Afirka don neman shawo kansu, da samun moriyar siyasa? Batun ba haka yake ba. Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya bayyana a wajen taron jiya cewa, “ Kasar Sin na son ganin gamayyar kasa da kasa sun ci gaba da mai da hankali kan kasashen Afirka, da nuna musu goyon baya.

Idan kasashen Afirka sun yarda, za a iya yin hadin kai tsakanin bangarori 3 ko fiye, a nahiyar Afirka. Kasashen Afirka suna bukatar wani yanayi na kwanciyar hankali da sada zumunta, maimakon ra’ayin yakin cacar baka, kana suna maraba da hadin gwiwar da zai amfani jama’a, maimakon shiga takarar wasu manyan kasashe.” Wannan magana ta nuna yadda bangaren Sin ke fahimtar ra’ayin kasashen Afirka.

Ta hanyar yin bincike kan tarihin hadin gwiwar Sin da Afirka, za mu iya fahimtar cewa, kasashen Afirka da kasar Sin, sun yi watsi da tunani na yakin cacar baka, wanda har yanzu kasashen yamma suke tsayawa a kai.

Sa’an nan sun juya ga tunanin al’ummar dan Adam mai makomar bai daya. Wanne ne daga cikin su zai fi amfanar al’ummun duniya?

Na san kowa zai iya ba da amsa.
Magance sabanin ra’ayi, da neman cimma matsaya, da kokarin hadin gwiwa don daidaita matsalolin da ake fuskanta, da neman samun hakikanin ci gaba, wannan shi ne ra’ayin da zai iya taimakawa, wajen kyautata yanayin da duniyarmu ke ciki, kuma babbar manufa ce da kasashen Afirka da kasar Sin ke tsayawa a kai, yayin da suke hadin gwiwa da juna. (Bello Wang)

Afirka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Lauya A Zamfara

'Yan Bindiga Sun Hallaka Lauya A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.