• English
  • Business News
Saturday, September 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

by Sulaiman
5 months ago
in Labarai
0
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamiɗo, murna bisa ƙaddamar da littafin tarihin rayuwar sa mai suna ‘Being True to Myself’, wanda aka yi a yau.

 

Shugaban Ƙasa ya bayyana littafin a matsayin muhimmin ƙari ga tarihin siyasar Nijeriya.

  • Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
  • Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, wanda ya wakilci Shugaban Ƙasar a wajen taron da aka gudanar a Cibiyar Taro ta NAF da ke Abuja, ya bayyana Lamiɗo a matsayin ɗan siyasa jarumi kuma mai aƙida wanda tafiyar rayuwar sa ta yi daidai da cigaban dimokiraɗiyyar Nijeriya.

 

Labarai Masu Nasaba

2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi

Idris ya ce: “Wannan ba kawai ƙaddamar da littafi ba ne, amma bikin rayuwa da jarumtaka, daidaito, da jajircewa ga tsarin dimokiraɗiyya suka bayyana.

 

“Ko da yake Alhaji Sule Lamiɗo babban jigo ne a jam’iyyar adawa kuma sau da dama mai suka ga gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu (GCFR), har yanzu yana daga cikin manyan ginshiƙai na cigaban siyasar Nijeriya.”

 

Ministan ya jaddada cewa Shugaba Tinubu ya yarda da siyasar da ke bai wa kowa dama, inda ake maraba da ra’ayoyi mabanbanta, kuma suna da muhimmanci ga tattaunawa kan makomar ƙasa.

 

“Kowane ɗan ƙasa, ba tare da la’akari da dangantakar sa da jam’iyya ba, yana da gurbin zama a teburin tattaunawa kan makomar ƙasa.”

 

Idris ya jinjina wa ƙoƙarin da Lamiɗo ya yi na fiye da shekaru goma wajen rubuta littafin, yana mai cewa ya taka rawar gani wajen adana tarihi, kuma ya buƙaci sauran tsofaffin ‘yan siyasa da su bi irin wannan hanya.

 

Ya kuma ce taken littafin, wato ‘Being True to Myself,’ ya dace da halayen Lamiɗo.

 

Ya ce: “Ya dace da halin Sule Lamiɗo da kuma sunan da yake da shi na ɗan siyasa mai aƙida da nuna ra’ayi kai-tsaye.

 

“Zan shawarci ɗalibai, malamai, ‘yan jarida, da sauran ‘yan siyasa da su karanta littafin don za su ga littafin yana da amfani a gare su na tsawon shekaru.”

 

Idris ya ƙara da cewa shi ma Shugaba Tinubu, kamar Lamiɗo, ya jajirce kan gaskiya, adalci, zaman lafiya da cigaban ƙasa.

 

Ya ce: “Ɗimbin ilimi da ƙwarewar marubucin, tabbas, wata baiwa ce da ya kamata duniya ta amfana da ita, kuma abin farin ciki ne ganin ya ɗauki mataki ya wallafa littafi.”

 

Yayin da Nijeriya take shirin cika shekaru 26 da dimokiraɗiyya, ministan ya bayyana cewa sauye-sauyen da gwamnatin Tinubu ke aiwatarwa – duk da yake masu tsauri ne – sun fara haifar da sakamako mai kyau a fannin tattalin arziki.

 

Ya ce: “Shin muna cewa mun kai inda ya kamata mu kai, kuma babu sauran aikin da ya rage? A’a, ko kaɗan. Abin da muke cewa mai sauƙi ne: cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya nuna ƙarfin hali da hangen nesa na musamman wajen ɗora Nijeriya a kan hanyar cigaba da bunƙasa na gaskiya.

 

“Kuma, bayan wata farawa mai ɗan wahala saboda tsauraran sauye-sauyen da ba za a guje masu ba, yanzu muna shiga wani sabon zamani na samun sakamakon alheri da aka yi niyya.”

 

Game da matsalar tsaro, ministan ya tabbatar da cewa Shugaban Ƙasa yana aiki tuƙuru wajen kare rayuka da ƙasa daga barazanar ‘yan ta’adda.

 

“Don haka muna son jaddada buƙatar a yaba da sadaukarwar da sojojin Nijeriya suke yi a wannan fanni,” inji shi.

 

Ya kuma bayyana cewa sababbin dokokin haraji da Shugaban Ƙasa ya gabatar suna nufin haɓaka kuɗaɗen shiga ga gwamnatoci a matakai daban-daban ba tare da ƙara wa talakawa nauyi ba.

 

“Shugaban Ƙasa yana maraba da suka mai ma’ana a kowane lokaci, cikin ruhin ’yancin faɗar albarkacin baki da dimokiraɗiyya, amma ba zai taɓa bari a karkatar da shi daga aikata abin da ya dace da Nijeriya ba.”

 

Manyan baƙi daga bangarori daban-daban na siyasa sun halarci taron don girmama tsohon gwamnan da kuma yin nazari kan gudunmawar da ya bayar wajen gina dimokiraɗiyya a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Next Post

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Related

2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC
Rahotonni

2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

7 hours ago
’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi

8 hours ago
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda
Labarai

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina: Nasara Ko Matsala?

9 hours ago
An Gano Cututtuka Uku Da Suka Ta Da Hankalin Hukumomin Lafiya A Nijeriya
Labarai

An Gano Cututtuka Uku Da Suka Ta Da Hankalin Hukumomin Lafiya A Nijeriya

10 hours ago
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru
Labarai

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Bincike A Kan Fashewar Wani Abu A Kaduna

13 hours ago
Trump Ya Haramta Wa Jami’an Nijeriya Masu Cin Hanci Da Rashawa Shiga Amurka
Labarai

Trump Ya Haramta Wa Jami’an Nijeriya Masu Cin Hanci Da Rashawa Shiga Amurka

14 hours ago
Next Post
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

LABARAI MASU NASABA

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

September 26, 2025
2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

September 26, 2025
Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI

Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI

September 26, 2025
’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi

September 26, 2025
Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

September 26, 2025
A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

September 26, 2025
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina: Nasara Ko Matsala?

September 26, 2025
Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa

Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa

September 26, 2025
An Gano Cututtuka Uku Da Suka Ta Da Hankalin Hukumomin Lafiya A Nijeriya

An Gano Cututtuka Uku Da Suka Ta Da Hankalin Hukumomin Lafiya A Nijeriya

September 26, 2025
Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Bayar Da Sabuwar Gudummawa Dangane Da Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya

Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Bayar Da Sabuwar Gudummawa Dangane Da Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya

September 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.