• English
  • Business News
Saturday, May 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

by Muhammad
9 hours ago
in Ilimi, Labarai, Zamantakewa
0
Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gamayyar Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban Jami’ar Bayero waɗanda suka kammala karatu a shekarar 2015 a Sashen Koyar da Harsuanan Nijeriya da Sashen Kimiyyar Harshe da Harsunan Ƙasashen Waje na Jami’ar, sun karrama abokin karatunsu da ya zama zakara wajen zama mutum na farko a ajin su da ya kammala digiri na uku a ɓangaren Kimiyyar Harshe, Dr. Sani Dauda Ibrahim.Ƙungiyar

Taron an gabatar da shi ranar Asabar 10, ga Mayu 2025 a dakin cin abinci da shaƙatawa na Albaik Chicken da ke titin zuwa Gwarzo a jihar Kano. A yayin taron walimar, tsofaffin ɗaliban sun karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim a matsayin gwarzo kuma wanda ya yi fice ajin 2015 da wata shaidar girmamawa ta musanman kan nuna ƙwazo wajen zama mutum na farko da tarihin ɗaliban ba zai manta da shi ba.

  • Tsofaffin Ɗaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan Naɗa Ma’ajin Hausawan Turai
  • Ɗaliban Jami’ar Bayero ‘Yan Ajin 2015 Sun Zamanantar Da Ɗakin Karatu Na M.A.Z Sani

A jawabin shugaban taron kuma Sakataren Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban, Muhammad Bashir Amin, ya godewa Allah bisa cikar burinsu na samun damar shirya walimar karrama abokin na su da ya yi fice a tsakaninsu tun lokacin da suke karatu tare da shi a matakin digirin farko a Jami’a, ya kuma yi fatan ci gaba da shirya makamancin irin wannan taruwa girmamawa ga mambobin ƙungiyar a fannonin rayuwa da dama, da fatan nasarar Dr. Sani Dauda Ibrahim ya samu ta amfani ilahirin ɗalibai da jami’ar da dukkan al’umma baki ɗaya, a jawabin nasa ya godewa shugaban Ƙungiyar Alhaji Hassan Baita Ubawaru (Ma’ajin Hausawan Turai) da ‘yan kwamitin shirya taron da sauran mambobin ƙungiyar kan irin haɗin kai da gudunmawar da suke bayarwa a koyaushe wajen ci gaban ƙungiyar.

Ƙungiyar
Mambobin Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Jami’ar Bayero lokacin da suke karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim

A nasa jawabin, Dr. Sani Dauda Ibrahim, ya nuna farin cikinsa tare da godewa shugabancin ƙungiyar bisa karrama shi da suka yi wajen shirya liyafar ta ya shi murna da suka yi, ya ce nasarar ba ta shi ce kaɗai ba, ta kowa da kowa, saboda tabbas bai san wahalar karatu ba saboda Allah ya shiga cikin lamarinsa sosai tare kuma da addu’a iyaye da dafawar malamansa da abokan karatunsa, ya kuma bayyana cewa a nasa ɓangaren ya ci alwashin ci gaba da bayar da tasa gudunmawar wajen ci gaban ƙungiya tare da tabbatar da dorewar zumunci a tsakanin mambobin ƙungiyar.

Dr. Tijjani Shehu Almajir a lokacin da ya ke miƙa kyautar karrama wa ga Dr. Sani Dauda Ibrahim
Dr. Tijjani Shehu Almajir a lokacin da ya ke miƙa kyautar karrama wa ga Dr. Sani Dauda Ibrahim

Shugaban Sashen Kimiyyar Harshe na Jami’ar Bayero, Dr. Tijjani Shehu Almajir, wanda shi ne ya jagoranci duba aikin Dr. Sani Dauda Ibrahim, ya bayyana ƙwazo da hazaƙar da ɗalibin ya ke da ita a matsayin wani abu da suke alfahari da shi.

Labarai Masu Nasaba

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

“Haƙiƙa muna alfahari da Dr. Sani Dauda Ibrahim da wannan ajin naku, musanman cewa akan ku na fara koyarwa a jami’a, kuma haɗin kan ‘yan wannan ajin ya zama na daban a cikin ƙungiyoyin tsofaffin ɗalibai, musanman saboda ayyuka da kuka gabatar na ci gaban ilimi a jami’ar Bayero da yadda kuke damuwar da al’amuran ilimi” cewar Dr. Almajir.

Taron ya samu halartar Dr. Maimuna Isma’il da ke koyarwa a sashen da sauran mambobin ƙungiya da ‘yan uwa da abokan arzikin Dr. Sani Dauda Ibrahim da aka karrama a wajen taron.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BUKHassan Baita UbawarukanoMuhammad Bashir AminReunionTsofaffin Ɗaliban Jami’ar BayeroUrwa Nigeria Limited
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

Next Post

An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

Related

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

12 hours ago
Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
Kananan Labarai

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

12 hours ago
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum
Labarai

‘Yan Ta’adda Na Amfani Da Na’urorin Zamani Daidai Lokacin Da Sojoji Ke Da Karancin Makamai -Zulum

14 hours ago
Dan Asalin Jihar Kano Ya Kafa Tarihin Kirkirar Manhaja Mai Auna Tsayin Bishiya A Faransa
Labarai

Dan Asalin Jihar Kano Ya Kafa Tarihin Kirkirar Manhaja Mai Auna Tsayin Bishiya A Faransa

15 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jaridar Da Ya Fallasa ‘Sharrin’ Da Ake Shirya Wa Natasha
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jaridar Da Ya Fallasa ‘Sharrin’ Da Ake Shirya Wa Natasha

15 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Labarai

Tinubu Ya Amince Da Lasisin Aikin Hakar Mai A Arewa

16 hours ago
Next Post
An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Bukaci Kada Amurka Ta Siyasantar Da Hadin Gwiwar Bangaren Ilimi

Sin Ta Bukaci Kada Amurka Ta Siyasantar Da Hadin Gwiwar Bangaren Ilimi

May 23, 2025
Kamfanoni Masu Jarin Waje Sun Ci Gajiyar Tsarin Kasar Sin Na Samar Da Rangwamen Gwamnati Ta Musayar Sabbin Kayayyaki Da Tsofaffi

Kamfanoni Masu Jarin Waje Sun Ci Gajiyar Tsarin Kasar Sin Na Samar Da Rangwamen Gwamnati Ta Musayar Sabbin Kayayyaki Da Tsofaffi

May 23, 2025
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

May 23, 2025
Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci

Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci

May 23, 2025
An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

May 23, 2025
Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

May 23, 2025
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

May 23, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

May 23, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

May 23, 2025
Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai

Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai

May 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.