ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsofaffin Ɗaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan Naɗa Ma’ajin Hausawan Turai

by Muhammad
2 years ago
Alh. Hassan Baita Ubawaru (Ma'ajin Hausawan Turai)

Alh. Hassan Baita Ubawaru (Ma'ajin Hausawan Turai)

Ƙungiyar Tsofaffin Ɗalibai na Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya da haɗin guiwar Tsofaffin ɗaliban Sashen Nazarin Kimiyyar Harshe na Jami’ar Bayero Kano ajin shekara ta 2015 ta miƙa sakon godiya ga Masarautar Hausawan Turai da ke birnin Paris na ƙasar Faransa da Mai Martaba Sarkin Hausawan Turai, Alhaji Sirajou Djankaɗo, bisa naɗi ɗan wannan ƙungiya kuma shugabanta, Alhaji Hassan Baita Ubawaru a matsayin Ma’ajin Hausawan Turai a ranar Lahadi 14 ga Yulin 2024.

Muhammad Bashir Aminu lokacin da yake miƙa wa Ma'ajin Hausawan Turai kyauta a madadin Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Jami'ar Bayero aji na 2015.
Ma’ajin Hausawan Turai, Alh. Hassan Baita Ubawaru, yana karbar kyauta daga Muhammad Bashir Aminu

Sakataren ƙungiyar, Muhammad Bashir Amin ne ya aike da wannan saƙon a madadin kungiyar ga Masarautar Hausawan Turai da Mai Martaba Alh. Sirajou Djankaɗo a wajen taron walimar taya murna da karramawa da abokan Mai girma Ma’ajin Hausawan Turai suka shirya masa a birnin Kano a ranar Litinin 29 ga Yulin 2024.

  • Za Mu Sabonta Dakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami’ar Bayero — Hassan Baita
  • Ɗaliban Jami’ar Bayero ‘Yan Ajin 2015 Sun Zamanantar Da Ɗakin Karatu Na M.A.Z Sani

A jawabin na Muhammad Bashir, ya ce tabbas an ajiye ƙwarya a gurbinta bisa zaɓo mutum mai nagarta da amana da hidimtawa a al’umma irin Alh. Hassan Baita Ubawaru, a wannan matsayi kuma uwa uba daman shi Hassan ɗin masani ne a fannin ilimin harshe da adabi da al’adun Hausawa don kuwa ya samu shaidar digirinsa na farko a harshen Hausa.

ADVERTISEMENT
Ma'ajin Hausawan Turai yana karbar kyauta daga Muhammad Bashir Aminu
Ma’ajin Hausawan Turai yana karbar kyauta daga Muhammad Bashir Aminu

“Haƙiƙa an karrama mu kuma mun ji daɗin wannan karamcin ƙwarai da gaske, kuma ƙungiya za ta ci gaba da ganin wannan karamcin har abada, za kuma mu kyautata alaƙa mai kyau da wannan Masarauta ta Hausawan Turai ta fuskar bunƙasa harshe da adabi da al’adun Hausawa da taimakon mabuƙata ” cewar Muhammad Bashir.

Sakataren ƙungiyar a ƙarshe ya aike da sakonsa na taya murna a madadin mambobin kungiyar ga sabon Ma’ajin Hausawan Turai, Alh. Hassan Baita Ubawaru, bisa naɗa shi a wannan matsayi na sarauta mai girma da Allah ya sa ya zama mutum na farko a tarihi da aka naɗa a Masarautar Hausawan Turai.

LABARAI MASU NASABA

Goron Juma’a

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

Bashir ya yi fatan Ma’ajin Turai ya ninka ayyukansa na alheri da ya saba da kuma yin haƙuri da hidimar jama’a da taimakon mabuƙata, ya kuma yi addu’ar Allah ya kama masa, ya taya shi riƙon kafa tarihi na alheri a wannan Masarauta mai girma.

Turai
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

GORON JUMA’A 17-04-2026
Goron Juma'a

Goron Juma’a

June 5, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
GORON JUMA’A 01-07-2025
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 22-05-2026

May 22, 2026
Next Post
Zanga-zanga: Shugaban Majalisa Ya Roki ‘Yan Nijeriya Su Kara Ba Wa Tinubu Lokaci 

Zanga-zanga: Shugaban Majalisa Ya Roki 'Yan Nijeriya Su Kara Ba Wa Tinubu Lokaci 

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.