ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsofaffin Ɗaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan Naɗa Ma’ajin Hausawan Turai

by Muhammad
2 years ago
Alh. Hassan Baita Ubawaru (Ma'ajin Hausawan Turai)

Alh. Hassan Baita Ubawaru (Ma'ajin Hausawan Turai)

Ƙungiyar Tsofaffin Ɗalibai na Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya da haɗin guiwar Tsofaffin ɗaliban Sashen Nazarin Kimiyyar Harshe na Jami’ar Bayero Kano ajin shekara ta 2015 ta miƙa sakon godiya ga Masarautar Hausawan Turai da ke birnin Paris na ƙasar Faransa da Mai Martaba Sarkin Hausawan Turai, Alhaji Sirajou Djankaɗo, bisa naɗi ɗan wannan ƙungiya kuma shugabanta, Alhaji Hassan Baita Ubawaru a matsayin Ma’ajin Hausawan Turai a ranar Lahadi 14 ga Yulin 2024.

Muhammad Bashir Aminu lokacin da yake miƙa wa Ma'ajin Hausawan Turai kyauta a madadin Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Jami'ar Bayero aji na 2015.
Ma’ajin Hausawan Turai, Alh. Hassan Baita Ubawaru, yana karbar kyauta daga Muhammad Bashir Aminu

Sakataren ƙungiyar, Muhammad Bashir Amin ne ya aike da wannan saƙon a madadin kungiyar ga Masarautar Hausawan Turai da Mai Martaba Alh. Sirajou Djankaɗo a wajen taron walimar taya murna da karramawa da abokan Mai girma Ma’ajin Hausawan Turai suka shirya masa a birnin Kano a ranar Litinin 29 ga Yulin 2024.

  • Za Mu Sabonta Dakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami’ar Bayero — Hassan Baita
  • Ɗaliban Jami’ar Bayero ‘Yan Ajin 2015 Sun Zamanantar Da Ɗakin Karatu Na M.A.Z Sani

A jawabin na Muhammad Bashir, ya ce tabbas an ajiye ƙwarya a gurbinta bisa zaɓo mutum mai nagarta da amana da hidimtawa a al’umma irin Alh. Hassan Baita Ubawaru, a wannan matsayi kuma uwa uba daman shi Hassan ɗin masani ne a fannin ilimin harshe da adabi da al’adun Hausawa don kuwa ya samu shaidar digirinsa na farko a harshen Hausa.

ADVERTISEMENT
Ma'ajin Hausawan Turai yana karbar kyauta daga Muhammad Bashir Aminu
Ma’ajin Hausawan Turai yana karbar kyauta daga Muhammad Bashir Aminu

“Haƙiƙa an karrama mu kuma mun ji daɗin wannan karamcin ƙwarai da gaske, kuma ƙungiya za ta ci gaba da ganin wannan karamcin har abada, za kuma mu kyautata alaƙa mai kyau da wannan Masarauta ta Hausawan Turai ta fuskar bunƙasa harshe da adabi da al’adun Hausawa da taimakon mabuƙata ” cewar Muhammad Bashir.

Sakataren ƙungiyar a ƙarshe ya aike da sakonsa na taya murna a madadin mambobin kungiyar ga sabon Ma’ajin Hausawan Turai, Alh. Hassan Baita Ubawaru, bisa naɗa shi a wannan matsayi na sarauta mai girma da Allah ya sa ya zama mutum na farko a tarihi da aka naɗa a Masarautar Hausawan Turai.

LABARAI MASU NASABA

Goron Juma’a

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

Bashir ya yi fatan Ma’ajin Turai ya ninka ayyukansa na alheri da ya saba da kuma yin haƙuri da hidimar jama’a da taimakon mabuƙata, ya kuma yi addu’ar Allah ya kama masa, ya taya shi riƙon kafa tarihi na alheri a wannan Masarauta mai girma.

Turai
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

GORON JUMA’A 17-04-2026
Goron Juma'a

Goron Juma’a

June 5, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
GORON JUMA’A 01-07-2025
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 22-05-2026

May 22, 2026
Next Post
Zanga-zanga: Shugaban Majalisa Ya Roki ‘Yan Nijeriya Su Kara Ba Wa Tinubu Lokaci 

Zanga-zanga: Shugaban Majalisa Ya Roki 'Yan Nijeriya Su Kara Ba Wa Tinubu Lokaci 

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.