• English
  • Business News
Saturday, June 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

by Sani Anwar
3 weeks ago
in Kananan Labarai
0
Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hon. Sanusi Ibrahim Yaro, Darakta Janar na Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu na kasa (STSG), ya bayyana cewa; nan ba jimawa ba, za su yi gangamin taronsu na kasa baki-daya.

“Za mu yi wannan gangamin taro ne, domin sake tabbatar da samun nasarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a karo na biyu, wanda muke sa ran aiwatar da taron nan da ‘yan wasu makwanni kadan masu zuwa,” in ji Yaro.

  • ‘Yan Ta’adda Na Amfani Da Na’urorin Zamani Daidai Lokacin Da Sojoji Ke Da Karancin Makamai -Zulum
  • Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jaridar Da Ya Fallasa ‘Sharrin’ Da Ake Shirya Wa Natasha

Ibrahim ya ci gaba da cewa, suna nan suna ci gaba da aiki babu dare babu rana, domin kuwa maganar da ake yi yanzu, dukkanin jihohin Arewacin wannan kasa da wasu daga cikin jihohin kudancin ƙasar nan, na nan suna shirya tarukansu daban-daban, kafin wannan babban taro da za a aiwatar na kasa a babban birnin tarayya Abuja.

“Tunda aka kafa wannan kungiya, ba mu yi kasa a gwiwa ba wajen tallata ayyuka da manufofin wannan gwamnati ga musamman ‘yan’uwanmu matasa maza da mata, don sanin irin kokarin da shugaban kasa ke yi na ciyar da wannan kasa gaba.”

Har ila yau, a cewar Hon. Yaro; sun yi wa wannan ƙungiya lakabi da sunan Seyi Tinubu (STSG) ne, saboda jajircewar Seyi Tinubun a kan matasa maza da mata.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya

Kazalika ya kara da cewa, idan za a iya tunawa, Seyi ya kewaya kusan dukkanin jihohin Arewacin kasa nan tare da tallafa wa al’umma da kayan abinci da kudade, musamman a watan Ramadana da ya gabata.

A karshe, Sanusi ya yi kira ga matasa maza da mata, kada su bari a bar su a baya a wannan tafiya, domin kuwa kungiya ta kowa da kowa ce, duk mai bukatar yin rajista; kofa a bude take, domin kuwa suna da ofisoshi a kowace jiha, ciki har da babban birnin tarayya Abuja da suke shirin bude kwanan nan ga masu bukatar shiga.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Seyi
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Ta’adda Na Amfani Da Na’urorin Zamani Daidai Lokacin Da Sojoji Ke Da Karancin Makamai -Zulum

Next Post

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

Related

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

2 months ago
Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya
Kananan Labarai

Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya

2 months ago
Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi

3 months ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Kananan Labarai

Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Dala Tiriliyan 7 A Tsarin Kasuwancin Musulunci Na Duniya

9 months ago
Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara
Labarai

Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara

9 months ago
Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Tallafawa Majinyata 1000 Da Abinci Da Kuɗi
Kananan Labarai

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Tallafawa Majinyata 1000 Da Abinci Da Kuɗi

9 months ago
Next Post
Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

LABARAI MASU NASABA

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

June 14, 2025
APC

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

June 14, 2025
Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

June 13, 2025
jam'iyyu

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

June 13, 2025
Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

June 13, 2025
Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

June 13, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

June 13, 2025
Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

June 13, 2025
Nijeriya Da Morocco Za Su Sanya Hannu Kan Kulla Yarjejeniyar Aikin Bututun Iskar Gas

Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida

June 13, 2025
Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

June 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.