ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Haraji

A halin da ake ciki yanzu haka, yanayin tattalin arzikin duniya na fuskantar guguwar rashin tabbas, a gabar da Amurka ke kara tsaurara matakan kakaba haraji kan hajojin da ake shigarwa kasar daga wasu kasashen duniya, matakan da masana tattalin arziki daga sassan kasa da kasa ke ta suka, tare da bayyana su a matsayin illa da ka iya dakile ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya, baya ga ingiza hauhawar farashi, da gurgunta tsarin cinikayyar kasa da kasa da hakan zai haifar.

Bisa halin da ake ciki, masu masana tattalin arziki na ganin matakan nan na kakaba karin haraji da Amurka ke aiwatarwa, za su ci gaba da zama barazana ga daidaiton tattalin arzikin duniya, kuma ko da kaso kadan daga cikin su Amurka ta aiwatar, hakan na iya tauye hasashen da aka yi na ci gaban tattalin arzikin duniya, tare da haifar da hauhawar farashi a Amurka ita kanta.

  • Kasar Sin Za Ta Kara Sanya Harajin Fito Na Kaso 34% Kan Dukkan Kayayyakin Da Take Shigowa Daga Amurka
  • Yadda Wata Gada Ta Balle Ta Kashe Mutum 60 A India

Idan mun duba irin wadannan matakai da Amurka ta dauka a baya, da wadanda take dauka a yanzu, ma iya cewa a wannan karo gwamnatin Amurka mai ci ta rungumi manufofi da tsare-tsare mafiya haifar da rashin tabbas sama da na kowane lokaci a baya, ta yadda lamarin ya zamo babban kalubale ga yanayin kasuwancin duniya.

ADVERTISEMENT

Wani abun lura ma shi ne yadda gwamnatin Amurka take ta kokarin dorawa kasar Sin laifinta na gazawa, da koma-bayan da take fuskanta ta fannin bunkasar tattalin arziki, zarge-zargen da ko shakka ba su da wata makama.

A daya hannun kuma, duk da cewa karin harajin na gwamnatin Amurka mai ci na iya rage givin cinikayya tsakaninta da Sin, amma kuma hakan zai haifar da karuwar givin cinikayya tsakanin Amurka da wasu karin kasashen duniya, wanda hakan zai sabbaba koma-baya ga tattalin arzikin duniya baki daya.

LABARAI MASU NASABA

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya

Masu fashin baki da dama na da ra’ayin cewa, tabbas illar wannan mataki na Amurka zai koma kanta, inda wasu daga sassan raya tattalin arzikin kasar kamar na albarkatun gona, da makamashi za su iya fuskantar matsin lamba mai tsanani.

Yayin da wasu sassan kamfanonin kasar kuma ka iya fuskantar raguwar ribar da suke samu da kaso mai yawa, sakamakon karin kudaden hajojin da ake samarwa a masana’antun kasashen da Amurkan ta karawa haraji.

La’akari da wadannan illoli, kamata ya yi Amurka ta yi karatun ta nutsu, ta dakatar da matakan kakaba haraji marasa ma’ana, kana ta koma teburin tattaunawa, domin warware duk wani savani na kasuwanci da cinikayya tare da dukkanin sassan da batun ya shafa, ta yadda za a gudu tare a tsira tare.

Haraji
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

MASU ALAKA

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi
Addini

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

May 2, 2026
Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya
Kananan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya

April 28, 2026
Wakili Ya Rasu Kwana 3 Da Karewar Wa’adinsa A Matsayin Dan Majalisar Dokokin Jihar Bauchi
Kananan Labarai

2027: Majalisar Dattawa Za Ta Ɗage Zaman Ta A Ranar Alhamis Saboda Zaɓen Fidda Gwani

April 28, 2026
Next Post
Bruno Fernandes Ba Na Sayarwa Ba Ne – Ruben Amorim

Bruno Fernandes Ba Na Sayarwa Ba Ne - Ruben Amorim

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.