‘Yansandan Kasar Portugal sun sanar da cewa an dawo da kofin gasar Zakarun Turai na mata bayan an sace shi a filin wasa na Jose Albalade da ke Lisbon, filin wasan nan ne za a buga wasan karshe da za a yi tsakanin masu rike da kofin gasar Barcelona da Arsenal.
Satar ta faru ne a lokacin wasan babbar gasar kasar Portugal tsakanin Sporting Lisbon da Bitoria Guimaraes ranar Asabar, amma ba a kai rahoto ga ‘yansanda ba sai washegari.
- Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba
- Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai
Wasu mutane da yawa sanye da rigunan balaclabas sun saka karfi wajen bude kofar wani gareji dake filin wasan, inda za a buga wasan karshen a yau Juma’a 24 ga watan Mayu inda suka yi awon gaba da kofin in ji ‘yansanda a cikin wata sanarwa da suka fitar ga manema labarai.
Baya ga kofin har wayau sun kuma tafi da wasu kayayyakin na hukumar UEFA, tuni dai aka mayar da wadannan kayayyaki tare da kofin ga hukumar kwallon kafar Turai, kamar yadda mai magana da yawun ‘yansandan ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP.
An gano mutum 13 da ake zargi dangane da satar a cewar sanarwar da ‘yansandan suka fitar, amma har yanzu ba a bayar da cikakken bayani kan aikin da ya kai ga kwato kayayyakin da aka sace ba, ana ci gaba da gudanar da bincike kuma rundunar ‘yansandan ta ce tana sa ran za ta kwato wasu kayayyaki tare da kara kama wasu karin masu laifin a cikin kwanaki masu zuwa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp