ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
11 months ago
PDP

Gwagwarmayar neman takarar shugaban kasa a jam’yyar PDP a 2027 ta kara kaimi tun bayan da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya fice daga jam’iyyar, wanda ta bude hanya ga gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, da sauran masu sha’awar neman takarar shugaban kasa da ke neman kalubalantar tazarcen Shugaban kasa Bola Tinubu.

Masu ruwa da tsaki na PDP, wadanda suka yi jawabi kan lamarin cikin sirri, sun tabbatar da cewa burin tsayawa takarar shugabancin kasar na Makinde da Bala ya kasance sanannen abu a tsakanin muhimman masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.

  • Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah
  • Matsalar Tsaro: Sarakuna Sun Bukaci Gwamnati Ta Canza Salo

Wata majiya mai tushe daga jam’iyyar ta bayyana cewa PDP ta bude kofa ga duk masu neman takarar shugaban kasa bisa bin dokokin jam’iyyar.

ADVERTISEMENT

Yayin da babban jigon jam’iyyar PDP, Cif Bode George, ya tabbatar a cikin wani tattaunawa ta musamman cewa, ana ci gaba da kokarin samun dan takarar shugaban kasa daga kudu, sauran mambobin kwamitin zartarwa na kasa sun bayyana ra’ayi daban-daban kan batun tsarin karba-karba na yankuna.

A daidai lokacin da PDP ke fama da rikicin cikin gida da suka hada da na shugabanci da batun tsarin karba-karba a tsakanin yankuna wanda jam’iyyar ke kokarin warwarewa kafin zaben 2027.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Kwanan nan jam’iyyar PDP ta gudanar da taron kwamitin zartarwa karo na 100 da aka gudanar ranar 30 ga Yuni, PDP ta warware rikicin da ya dade yana ci mata tuwo a kwarya na batun mukamin sakataren jam’iyyar na kasa wanda ta tabbatar da Sanata Samuel Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyyar.

Duk da wannan warware batun, Atiku da wasu magoya bayansa sun fice daga jam’iyyar sakamakon rashin warware rikicin gida na jam’iyyar.

A ranar 1 ga Yuli, Atiku da Peter Obi da Rotimi Amaechi da Nasir El-Rufai, da wasu sun kulla hadaka a karkashin jam’iyyar ADC, sun ce sun yi wannan hadakar ne domin kalubalantar APC a zaben 2027.

A matsayin wani bangare na wannan yunkurin hadin gwiwa, sun nada tsohon shugaban majalisar dattawa, Dabid Mark a matsayin shugaban jam’iyyar na kasa na wucin gadi da tsohon gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola a matsayin sakataren jam’iyyar na kasa na wucin gadi.

Majiya mai tushe ta tabbatar da cewa Makinde da Bala Mohammed su ne manyan ‘yan takarar shugaban kasa a jam’iyyar a yanzu haka, yayin da ake sa ran wasu jiga-jigan jam’iyyar za su biyo baya kafin zaben 2027.

Majiyar ta ce, “Ana tambayar game da wadanda suka nuna sha’awarsu na neman tikitin takarar shugaban kasa a jam’iyya a halin yanzu. Duk da dai ba su fito fili sun bayyana ba, mun ji daga wurin shugabannin jam’iyyar, cewa Makinde da Bala Mohammed har ma da wasu tsoffin gwamnonin daga Kudu suna da sha’awar neman tikitin shugaban kasa jam’iyyar PDP a 2027.

“Amma a hakikanin gaskiya, a yanzu haka ba za mu iya sanin adadin wadanda suke sha’awar tsayawa takarar shugaban kasa a PDP, sai idan lokaci ya yi duk za a san su. Don haka, jam’iyyar PDP ta bude kofarta ga kowa, kuma ta kasance jam’iyyar da ke da karbuwa sosai a tsakanin ‘yan Nijeriya.”

Wani jigo a jam’iyyar wanda ya nemi a Sakaye sunansa don ba a shi izinin yin magana a hukumance ba, ya goyi bayan bude tikitin takarar shugaban kasa a PDP a 2027 ga dukkan ‘yan Nijeriya.

Shi kuwa, tsohon mataimakin shugaban PDP na yankin kudu maso yammaci, Eddy Olafeso, ya bayyana cewa shugabannin jam’iyyar sun dauki darashi ga abubuwan da suka faru a baya.

Yayin da tsohon sakataren jam’iyyar na kasa, Ibrahim Tsauri, ya shawarci mambobin jam’iyyar cewa su bar uwar jam’iyyar ta yanke hukunci, sannan kuma ya yi gargadi kan kauce wa bin tsarin karba-karba.

A nasa martanin, daraktan yada labarai na jam’iyyar APC, Bala Ibrahim ya ce Shugaban Tinubu zai kayar da Makinde, Bala Mohammed, ko wani dan takarar da PDP ta tsaida a 2027.

Ibrahim ya bayyana cewa, “Makinde da Bala Mohammed ba su da wata gogewa a matakin kasa na siyasar Nijeriya. Wadannan gwamnonin biyu ba za su iya jure fafatawar siyasar kasa nan ba. Ba su da gogewar da dan takararmu yake da shi.

“Mutane da ka ambata ba su da ikon doke shugaban kasa a kowanne fanni na siyasa. Wannan ba matsala ce da za ta ba mu ciwon kai ba. Koma dai wane yanki PDP zai fitar da dan takarar shugaban kasa ba zai yi nasara ba a 2027.”

 

PDP
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
PDP
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Sulaiman
    Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin
  • Sulaiman
    Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci
  • Sulaiman
    Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da "Kauracewar" Amurka

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.