Jami’an hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) tare da hadin gwiwar sojojin Nijeriya sun kashe ‘yan bindiga fiye da 45 a garin Kuchi da ke karamar hukumar Munya ta jihar Neja.
Majiyoyin tsaro sun shaidawa LEADERSHIP cewa, farmakin da aka gudanar a cikin sirri, ya kara nuna wata nasara a hare-haren da ake ci gaba da kai wa ‘yan ta’adda a yankin.
- Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa
- Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa
Majiyar ta bayyana cewa, hukumar ta DSS ta bi sahun ‘yan ta’addan inda ta dakile hare-haren su a kauyukan, wanda kasurgumin fitaccen shugaban ‘yan bindiga, Dogo Gide da sauran ‘yan bindiga da ke masa biyayya suka shirya kai wa al’ummomi a yankin.
Kamar yadda majiyar ta bayyana, bayanan sirri da hukumar DSS ta samu sun nuna cewa, ‘yan ta’addan da suka fito daga dajin Bilbis da ke karamar hukumar Maru ta jihar Zamfara da wasu sassan jihar Kaduna, Gide ne ya gayyace su da su kai farmaki a kauyukan Kuchi.
Majiyar ta ci gaba da cewa, “da sanyin safiyar ranar Litinin, 2 ga watan Yuni 2025, ‘yan bindiga daga jihohin Kaduna da Zamfara, wadanda yawansu ya kai 100, dauke da muggan makamai, sun nufi garin Kuchi da ke karamar hukumar Munya.
“Amma jami’an tsaro, suka yi musu kwanton bauna a wani hari na bazata inda suka tarwatsa ‘yan ta’addan a wajen garin Kuchi, inda suka yi nasarar fatattakar ‘yan bindigar, tare da jikkata wasu da dama, tare da kwato babura da alburusai.”
A halin da ake ciki, rahotanni sun kuma nuna cewa, biyar daga cikin jami’an DSS sun samu munanan raunuka kuma a halin yanzu suna kwance a asibiti.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp