• English
  • Business News
Sunday, September 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani and Sulaiman
4 months ago
in Dausayin Musulunci
0
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Assalamu alaikum wa ramtullahi ta’ala wa barkatuh. Masu karatu idan ba ku manta ba, a makon da ya gabata mun tsaya ne a wurin da Manzon Allah (SAW) ya ce wa Sahabbai duk wanda bai zo da abin hadaya ba ya warware hajjinsa ya mayar da shi umura. Za mu ci gaba.

Sahabbai suka ce “Ya Rasulallahi bai fi kwana hudu a yi Arfa ba”, Annabi (SAW) ya ce “Ku cire haramar kawai, ku yi aski.”

  • Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi
  • Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

“Sai Surakatu Ibn Malik Ibn Ju’ushamu ya mike ya ce “Ya Rasulallahi, wannan hukunci na yanzu (na mayar da Hajji Umura saboda rashin zuwa da abin hadaya), na wannan shekarar ne kawai ko na ko wace shekara ne?”, sai Annabi (SAW) ya shigar da yatsunsa wasu a cikin wasu ya dunkule su ya ce “Umura ta shiga cikin Hajji sau biyu, bari ma dai Umura ta shiga cikin Hajji har abada.” Sai Sayyidina Aliyu (RA) ya zo daga Yeman da rakuma, yana zuwa ya shiga wurin iyalinsa, ya tarad da matarsa (Sayyida Fadima (AS)) ta yi ado, ya tambaye ta game da hakan alhali ta riga ta yi harama da Hajji? Sai ta ce ma sa: “Babana (SAW) ya ce in yi.” Sayyidina Aliyu ya fada mana a Iraki (in ji Jabir) cewa, “Sai na tafi wurin Babanta don na kai kararta bisa abin da ta aikata kuma in tambaye shi (SAW). Da na fada ma sa, sai Annabi (SAW) ya ce “ta yi gaskiya, ta gaskiya. Kai me ka ce da za ka yi haramar Hajji?” sai na ce, “Cewa na yi; na yi niyyar harama da abin da Annabi ya yi harama da shi.”, daga nan Annabi (SAW) ya ce “Ni ina da abin hadaya, don haka ba zan warware harama ba”. Sayyidina Aliyu ya ce “to nima na zo da rakuma” sai Annabi (SAW) ya ce “to ka shiga cikin hadayata”, sai adadin rakuman da Annabi ya zo da su da wanda Sayyidina Aliyu ya zo da su suka kai yawan guda 100. Daga nan mutanen (da ba su zo da abin hadaya ba) duk suka warware Hajjinsu sai Annabi (SAW) kawai da wadanda suka zo da abin hadayarsu (Sayyidina Aliyu da wani Sahabi guda daya).

“Haka aka zauna har zuwa ranar takwas ga wata, sai Manzon Allah (SAW) ya hau rakumarsa zuwa Mina inda ya yi Sallolin Azahar, La’asar, Magriba, Isha’i, Asubahi duk a can. Da gari ya waye bayan rana ta fito, Annabi (SAW) ya yi umurnin cewa a je a kafa ma sa rumfarsa a Arfa. Annabi (SAW) ya tafi Arfa ya shiga cikin rumfarsa, bai fito ba har sai lokacin da rana ta gota, sai ya bukaci a dora wa rakumarsa sirdi, ya hau aka biyo bayansa zuwa kwarin nan (wurin da Masallacin Namira yake a yanzu) ya yiwa mutane huduba… Bayan ya kammala sai Bilal ya yi wazna aka fara Sallah. Annabi (SAW) ya hada Azuhur da La’asar (Kasaru), daga nan ya hau rakuminsa ya dawo Arfa. Ya kalli Alkibla ya yi ta Zikiransa yana tsaye har zuwa lokacin da rana ta fadi. Sai ya sa Usamatu Ibn Zaidu ya hau bayansa a kan rakuminsa ya kama hanya yana tafiya ba tare da sauri ba yana mai nuni da hannunsa cewa mutane su tafi sannu a hankali, har aka zo Muzdalifa. Annabi (SAW) ya yi mana Magriba da Isha’i da kiran sallah daya, ikama guda biyu amma Isha’i kasru aka yi. Ana kammala sallar sai Annabi (SAW) ya kwanta ba tare da ya yi nafila ko daya ba har zuwa Asalatu. Sannan ya tashi ya yiwa al’umma Sallar Asubahi.

“Daga nan ya hau rakumarsa zuwa Mash’aril Haram (wani Masallaci kafin isa wurin Jifan Shaidan). Ya tsaya a nan yana Kabbarbari har zuwa lokacin da gari ya yi sarari, sannan ya mika hanya inda ya goyo Fadlu Dan Abbas a rakuminsa… Har suka iso Badnil Muhassar (wurin da aka hallaka giwaye) inda ya dan yi sauri har ya shige wurin ya bi ta hanyar da ake isa wurin Jifar Jamratul Akba ya yi Jifa da tsakuwa bakwai. Sannan bayan ya yi addu’a sai ya tafi wurin hadayarsa ya soke rakumi 63 da hannunsa, sai ya mika wa Sayyidina Aliyu mashi ya soke ragowar. Kuma ya yi horo a yanko nama kadan a ko wane rakumi aka dafa ya ci. Daga nan ya yi aski, sai kuma ya hau abin hawansa zuwa Makka ya yi Dawafin saukowa daga Arfa (Dawaful Ifada). Sannan ya yi Safa da Marwa. Bayan ya kammala sai ya je Rijiyar Zamzam, ‘ya’yan Abdulmuddalibi suka bashi guga ya sha.” Wannan shi ne ruwayar Hajjin Annabi (SAW) da Sayyidina Jabiru (RA) ya ruwaito.

Labarai Masu Nasaba

Muna Murna Da Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (1)

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah

Malamai sun yi bayanin cewa a cikin wannan Hadisin akwai hukunce-hukuncen Aikin Hajji sama da guda 100 a ciki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Next Post

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Related

Manzon Allah
Dausayin Musulunci

Muna Murna Da Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (1)

2 weeks ago
Kyawawan Abubuwa Da Allah Ya Yi Wa Manzon Allah (SAW) Na Girmamawa
Dausayin Musulunci

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah

3 weeks ago
Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (7)
Dausayin Musulunci

Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (7)

4 weeks ago
Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (6)
Dausayin Musulunci

Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (6)

1 month ago
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)
Dausayin Musulunci

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

1 month ago
Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa
Dausayin Musulunci

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa

2 months ago
Next Post
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

LABARAI MASU NASABA

Kin Amincewar Japan Game Da Muggan Laifukan Yakin Da Ta Aikata Ya Dakatar Da Bukatar Sin Ga Hukumar UNESCO

Kin Amincewar Japan Game Da Muggan Laifukan Yakin Da Ta Aikata Ya Dakatar Da Bukatar Sin Ga Hukumar UNESCO

September 20, 2025
An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya

An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya

September 20, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Martaba Hakkokin Kamfanoni

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Martaba Hakkokin Kamfanoni

September 20, 2025
Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

September 20, 2025
Shugaban Kasar Iran Ya Yi Tsokaci Kan Shawarar Tsarin Inganta Jagorancin Duniya

Shugaban Kasar Iran Ya Yi Tsokaci Kan Shawarar Tsarin Inganta Jagorancin Duniya

September 20, 2025
Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

September 20, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

September 20, 2025
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

September 20, 2025
Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

September 20, 2025
Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

September 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.