ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani and Sulaiman
1 year ago
Aikin hajji

Assalamu alaikum wa ramtullahi ta’ala wa barkatuh. Masu karatu idan ba ku manta ba, a makon da ya gabata mun tsaya ne a wurin da Manzon Allah (SAW) ya ce wa Sahabbai duk wanda bai zo da abin hadaya ba ya warware hajjinsa ya mayar da shi umura. Za mu ci gaba.

Sahabbai suka ce “Ya Rasulallahi bai fi kwana hudu a yi Arfa ba”, Annabi (SAW) ya ce “Ku cire haramar kawai, ku yi aski.”

  • Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi
  • Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

“Sai Surakatu Ibn Malik Ibn Ju’ushamu ya mike ya ce “Ya Rasulallahi, wannan hukunci na yanzu (na mayar da Hajji Umura saboda rashin zuwa da abin hadaya), na wannan shekarar ne kawai ko na ko wace shekara ne?”, sai Annabi (SAW) ya shigar da yatsunsa wasu a cikin wasu ya dunkule su ya ce “Umura ta shiga cikin Hajji sau biyu, bari ma dai Umura ta shiga cikin Hajji har abada.” Sai Sayyidina Aliyu (RA) ya zo daga Yeman da rakuma, yana zuwa ya shiga wurin iyalinsa, ya tarad da matarsa (Sayyida Fadima (AS)) ta yi ado, ya tambaye ta game da hakan alhali ta riga ta yi harama da Hajji? Sai ta ce ma sa: “Babana (SAW) ya ce in yi.” Sayyidina Aliyu ya fada mana a Iraki (in ji Jabir) cewa, “Sai na tafi wurin Babanta don na kai kararta bisa abin da ta aikata kuma in tambaye shi (SAW). Da na fada ma sa, sai Annabi (SAW) ya ce “ta yi gaskiya, ta gaskiya. Kai me ka ce da za ka yi haramar Hajji?” sai na ce, “Cewa na yi; na yi niyyar harama da abin da Annabi ya yi harama da shi.”, daga nan Annabi (SAW) ya ce “Ni ina da abin hadaya, don haka ba zan warware harama ba”. Sayyidina Aliyu ya ce “to nima na zo da rakuma” sai Annabi (SAW) ya ce “to ka shiga cikin hadayata”, sai adadin rakuman da Annabi ya zo da su da wanda Sayyidina Aliyu ya zo da su suka kai yawan guda 100. Daga nan mutanen (da ba su zo da abin hadaya ba) duk suka warware Hajjinsu sai Annabi (SAW) kawai da wadanda suka zo da abin hadayarsu (Sayyidina Aliyu da wani Sahabi guda daya).

ADVERTISEMENT

“Haka aka zauna har zuwa ranar takwas ga wata, sai Manzon Allah (SAW) ya hau rakumarsa zuwa Mina inda ya yi Sallolin Azahar, La’asar, Magriba, Isha’i, Asubahi duk a can. Da gari ya waye bayan rana ta fito, Annabi (SAW) ya yi umurnin cewa a je a kafa ma sa rumfarsa a Arfa. Annabi (SAW) ya tafi Arfa ya shiga cikin rumfarsa, bai fito ba har sai lokacin da rana ta gota, sai ya bukaci a dora wa rakumarsa sirdi, ya hau aka biyo bayansa zuwa kwarin nan (wurin da Masallacin Namira yake a yanzu) ya yiwa mutane huduba… Bayan ya kammala sai Bilal ya yi wazna aka fara Sallah. Annabi (SAW) ya hada Azuhur da La’asar (Kasaru), daga nan ya hau rakuminsa ya dawo Arfa. Ya kalli Alkibla ya yi ta Zikiransa yana tsaye har zuwa lokacin da rana ta fadi. Sai ya sa Usamatu Ibn Zaidu ya hau bayansa a kan rakuminsa ya kama hanya yana tafiya ba tare da sauri ba yana mai nuni da hannunsa cewa mutane su tafi sannu a hankali, har aka zo Muzdalifa. Annabi (SAW) ya yi mana Magriba da Isha’i da kiran sallah daya, ikama guda biyu amma Isha’i kasru aka yi. Ana kammala sallar sai Annabi (SAW) ya kwanta ba tare da ya yi nafila ko daya ba har zuwa Asalatu. Sannan ya tashi ya yiwa al’umma Sallar Asubahi.

“Daga nan ya hau rakumarsa zuwa Mash’aril Haram (wani Masallaci kafin isa wurin Jifan Shaidan). Ya tsaya a nan yana Kabbarbari har zuwa lokacin da gari ya yi sarari, sannan ya mika hanya inda ya goyo Fadlu Dan Abbas a rakuminsa… Har suka iso Badnil Muhassar (wurin da aka hallaka giwaye) inda ya dan yi sauri har ya shige wurin ya bi ta hanyar da ake isa wurin Jifar Jamratul Akba ya yi Jifa da tsakuwa bakwai. Sannan bayan ya yi addu’a sai ya tafi wurin hadayarsa ya soke rakumi 63 da hannunsa, sai ya mika wa Sayyidina Aliyu mashi ya soke ragowar. Kuma ya yi horo a yanko nama kadan a ko wane rakumi aka dafa ya ci. Daga nan ya yi aski, sai kuma ya hau abin hawansa zuwa Makka ya yi Dawafin saukowa daga Arfa (Dawaful Ifada). Sannan ya yi Safa da Marwa. Bayan ya kammala sai ya je Rijiyar Zamzam, ‘ya’yan Abdulmuddalibi suka bashi guga ya sha.” Wannan shi ne ruwayar Hajjin Annabi (SAW) da Sayyidina Jabiru (RA) ya ruwaito.

LABARAI MASU NASABA

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

Malamai sun yi bayanin cewa a cikin wannan Hadisin akwai hukunce-hukuncen Aikin Hajji sama da guda 100 a ciki.

Aikin hajji
Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
+ posts Bio
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Falalar Neman Tsari Daga Sharrin Shaidan
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Bukatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
Aikin hajji
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a
  • Sulaiman
    Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
  • Sulaiman
    Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje
Dausayin Musulunci

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

July 3, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)
Dausayin Musulunci

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Manzon Allah
Dausayin Musulunci

Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha

June 19, 2026
Next Post
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

July 7, 2026
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.