Kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin Jiang Bin, ya ce Sin na jan kunnen mahukuntan jam’iyyar DPP mai mulkin yankin Taiwan, da cewa makaman Amurka ba za su tseratar da su ba, kuma duk wani mataki na yunkurin neman ‘yancin Taiwan ba zai yi nasara ba.
Jiang Bin ya bayyana hakan ne a Litinin din nan, yayin da yake amsa tambayar manema labarai, dangane da rahotannin dake cewa, Amurka na dakon wasu sabbin nau’o’in tankokin yaki samfurin M1A2 zuwa Taiwan, tare da shirin fadada yawan makaman da take sayarwa Taiwan din cikin shekaru hudu masu zuwa.
Jiang ya kara da cewa, batun Taiwan muhimmin lamari ne cikin jerin moriyar kasar Sin, kuma shi ne jan layi na farko da ba za a amince a tsallaka shi ba cikin alakar Sin da Amurka.
Jami’in ya ce, “Muna kira ga tsagin Amurka da ya dakatar da duk wani nau’in hadin gwiwar ayyukan soji da Taiwan, in ba haka ba, wuta za ta kona su, kuma matakan da suka dauka ba za su haifar da komai ba sai illata moriyarsu. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp