Matatar Dangote ta sanar da cewa zata fara rarraba man fetur (PMS) da dizal a duk faɗin Nijeriya tun daga ranar 15 ga Agusta, 2025. Wannan shiri zai baiwa masu sayarwa, da ‘yan kasuwa, da masana’antu da sauran manyan masu amfani damar siye kai tsaye daga kamfanin.
Don inganta hanyoyin rarrabawa, Dangote ya ƙaddamar da sabbin tankokin iskar gas (CNG) guda 4,000 da kuma gina tashoshin CNG. Wannan tsarin zai rage farashin sufuri da kuma taimakawa wajen rage farashin kayayyaki masu amfani da man fetur.
- Aliko Dangote Ya Sauka Daga Shugabancin Kamfanin Sukarin Dangote
- Nan Ba Da Jimawa Ba Harkar Man Fetur Za Ta Sauya A Nijeriya – Dangote
Kamfanin ya kuma bayar da damar bashi ga ‘yan kasuwa masu siyan lita 500,000, inda za su iya samun ƙarin lita 500,000 a kan bashi na tsawon makonni biyu. Wannan shiri na sauke farashin man fetur zai taimaka wajen rage hauhawar farashin kayayyaki da bunƙasa tattalin arziki.
Sanarwar ta nuna cewa wannan shiri ya yi daidai da shirin “Renewed Hope Agenda” na Shugaba Bola Tinubu. An buƙaci masu sha’awar shiga wannan shirin su yi rijista tsakanin ranar 16 ga Yuni zuwa 15 ga Agusta.
Dangote Refinery ya ce wannan shiri na daga cikin ƙoƙarinsa na taimakawa wajen samar da man fetur mai arha a Nijeriya, wanda zai inganta rayuwar al’umma da tattalin arzikin kasar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp