Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa mai kula da yankin Arewa maso Gabas, Mustapha Salihu, ya bayyana dalilin da ya sa ya mara wa Shugaba Bola Tinubu baya domin sake tsayawa takara a 2027 ba tare da ambaton Mataimakin Shugaba Ƙasa, Kashim Shettima, a jawabinsa ba.
Jawabin nasa ya janyo ce-ce-ku-ce a taron shugabannin APC na Arewa maso Gabas da aka yi a Jihar Gombe.
- ‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano
- Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga
Yayin wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels, Salihu ya ce ba a fahimce shi ba ne, kuma kafafen yaɗa labarai sun bayar da rahoton ba daidai ba.
“Wannan matsala ta faru ne saboda yadda aka yi wa jawabina fassara ba daidai ba. Da an saurari jawabin gaba ɗaya, musamman ƙarshensa, da an ji na yaba wa Mataimakin Shugaban Ƙasa,” in ji shi.
Salihu ya ce kafin ya nemi a goyi bayan Tinubu ya sake tsayawa takara, ya fara da yaba wa Shettima da sauran ‘yan yankin Arewa maso Gabas da aka ba su manyan muƙamai a gwamnati.
“Na ce Shettima ɗanmu ne, kuma muna alfahari da shi. Na kuma gode wa Tinubu bisa yadda ya bai wa ‘yan Arewa maso Gabas muƙamai masu gwaɓi kafin na nemi a mara masa baya,” in ji Salihu.
A lokacin taron, wasu matasa sun kusan kai masa hari, amma ya ce hakan ya faru ne saboda wasu ba su fahimci abin da ya yi ba.
Ya kuma jaddada cewa a tsarin jam’iyya, mutum ɗaya ne kawai ake zaɓa a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa a lokacin zaɓen fidda gwani, kuma shi ne ke da ‘yancin zaɓar mataimakinsa.
“Ba a daidaita tikitin shugaba da mataimaki a zaɓen fidda gwani. Ɗan takara kawai ake zaɓa, kuma yana da ‘yancin zaɓar wanda zai mara masa baya,” in ji shi.
Salihu ya kuma ƙaryata jita-jitar cewa akwai saɓani tsakanin Tinubu da Shettima.
Ya zargi wasu da ya kira “’yan kasuwar rikici” da ƙoƙarin ɓata lamarin domin amfanin kansu.
“Waɗanda ke yaɗa irin waɗannan labarai suna neman cin moriyar rikicin ne. Ba a gudanar da harkokin jam’iyya a dandalin sada zumunta ko a jaridu ba, a ofishin jam’iyya ake yin hakan,” in ji shi.
A ƙarshe, Salihu ya roƙi mambobin jam’iyyar da al’umma su guji yarda da jita-jita, yana mai cewa jam’iyyar APC na nan daram, babu wata matsala.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp