Masarautar Gaya da ke Jihar Kano ta ƙwace sarautar Wazirin Gaya daga hannun Alhaji Usman Alhaji.
Sanarwar hakan ta fito ne cikin wata wasiƙar da aka aike masa, kamar yadda Jami’in Yaɗa Labarai na Masarautar Gaya, Munzali Muhammad Hausawa, ya bayyana wa manema labarai.
- Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro
- Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi
Sakataren Masarautar Gaya, Alhaji Bello Halilu, ya gode wa Alhaji Usman bisa gudunmawar da ya bai wa masarautar.
“Masarauta na godiya ƙwarai da gaske bisa sadaukarwarsa, goyon baya ga masarauta da ƙoƙarin raya al’adun Gaya,” in ji shi.
Alhaji Usman ya samu sarautar Wazirin Gaya ne a ranar 26 ga watan Janairu, 2020, bayan ya yi aiki a matsayin Sakataren Gwamnatin Jihar.
Kafin wannan, yana riƙe da sarautar Walin Gaya, wanda aka ba shi lokacin da gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje ta ƙirƙiri sabbin masarautu.
Masarautar ta ce an ɗauki wannan matakin ne domin kare mutunci da ƙimar sarautun gargajiya bisa tsarin da aka gada.
Sai dai matakin ya zo ne mako guda bayan Alhaji Usman ya soki gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf, kan zarginta da karɓar bashi na dala miliyan 6.6.
Gwamnatin Kano ta musanta zarge-zargen, tana mai cewa ba gaskiya ba ne face tsantsar siyasa.
Ko da yake masarautar ba ta danganta ƙwace sarautar da wannan suka da Alhaji Usman ya yi ba, lokacin da aka ɗauki matakin ya haifar da zargi da cece-kuce a tsakanin jama’a.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp