Dan majalisar dattawa mai wakiltar Neja ta Arewa, Sanata Abubakar Sani Bello, ya yi Allah wadai da mummunan harin da ‘yan bindiga suka kai kan wasu al’ummomi a karamar hukumar Mariga ta jihar Neja.
Sanata Bello wanda shi ne Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Harkokin Waje, ya bayyana maharan a matsayin “Makiyan zaman lafiya”.
Harin wanda ya afku a ranar Talata, 24 ga watan Yuni, 2025, a yankin Gulbin Boka da Mangoro dake Bangi, ya yi sanadin mutuwar jami’an sojojin Nijeriya 17.
Bello, a wata sanarwa da ya fitar ta hannun mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Muawiyah Yusuf, ya bayyana matukar bacin ransa da alhininsa kan wannan mummunan harin.
Sanata Bello wanda kuma tsohon gwamnan jihar Neja ne, ya yi jinjina ga sojojin da suka rasa rayukansu a bakin aiki, inda ya bayyana su a matsayin jarumai na kasa wadanda suka sadaukar da rayuwarsu domin kare zaman lafiya da ‘yancin Nijeriya.
Ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan sojojin da suka rasu, yana mai addu’ar Allah ya kara musu lafiya, ya basu hakurin juriya da irin wannan rashi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp