• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

by Rabi'u Ali Indabawa
4 months ago
Neja

Hukumar Ba Da Agajin Gaggawa Ta Jihar Neja, NSEMA, ta ce sama da mutane 410 ne suka mutu a wasu Ibtila’i da suka faru a jihar daga shekarar 2024 zuwa yau. Darakta Janar na Hukumar, Alhaji Abdullahi Arah ne ya bayyana haka a zantawarsa da manema labarai a ofishinsa da ke Minna, jiya.

Arah, ya ce duk da kalubale iri-iri da aka samu a wannan lokacin, ma’aikatan suna yin iyaka kokarinsu wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyan NSEMA yadda ya kamata ta hanyar halartar abubuwan gaggawa daban-daban a fadin jihar.

  • Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
  • Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

A cewarsa, Ibtilala’i na farko da aka samu a 2024 shi ne fashewar tankar mai a Agaie, shalkwatar Karamar Hukumar Agaie wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 60, mutane takwas suka jikkata.

Babban daraktan ya bayyana cewa fashewar tankar mai ta Dikko wacce ta afku a ranar 18 ga watan Janairu, ta yi sanadin mutuwar mutum sama da 80, inda ya kara da cewa a tsawon wannan lokaci hukumar na hadin gwiwa da ma’aikatan lafiya tare da tura tawagar gaggawa domin shawo kan lamarin.

Akan tashin bam din da aka samu a Sabon Pegi da ke Karamar Hukumar Mariga, ya ce mutane biyu ne kawai suka mutu, yayin da gidaje da dama suka ruguje. Gwamnati ta bayar da kayan agaji da kudade ga wadanda abin ya shafa. “Na baya-bayan nan shi ne bala’in ambaliyar ruwa na Mokwa wanda ya raba dubban mutane da gidajensu, yayin da mutum 270 suka rasa rayukansu.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NASENI

Daɓid Adeyemi

Hukumar ta NSEMA ta jagoranci gudanar da aikin, tare da tattara kayan aiki gami da tura kungiyoyin bayar da agajin gaggawa tare da hadin gwiwar hukumomin kananan hukumomi.’ Arah, ya bayyana cewa, kafin lokacin damina, hukumar ta NSEMA ta kaddamar da shirin wayar da kan jama’a game da ambaliyar ruwa a duk shekara a matsayin gangamin gargadin farko a ma’aikatun masarautu takwas, da nufin kara wayar da kan jama’a.

“NSEMA ta kuma bayar da agaji ga wadanda gobarar gidaje da kasuwanci ta shafa a sassan jihar”.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Labarai

Hukumar NASENI

October 25, 2025
Labarai

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka
Kiwon Lafiya

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025
Next Post
NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Na 15

Kasar Sin Ta Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Na 15

October 25, 2025
Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

October 25, 2025
An Kaddamar Da Nuna Muhimman Shirye-shiryen CMG A Membobin APEC

An Kaddamar Da Nuna Muhimman Shirye-shiryen CMG A Membobin APEC

October 25, 2025
Zuwan Tsoffin ’Yan Wasan Barcelona Abuja Ya Nuna Ana Samun Zaman Lafiya A Nijeriya – Matawalle

Zuwan Tsoffin ’Yan Wasan Barcelona Abuja Ya Nuna Ana Samun Zaman Lafiya A Nijeriya – Matawalle

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Lafiya Na Shekarar 2025 Dakta Seidu Adebayo Bello

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.