ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
NUC

Sakataren Zartarwa na Hukumar Kula da Jami’o’i ta Kasa (NUC), Farfesa Abdullahi Yusuf Ribadu, ya bukaci jami’o’in Nijeriya da su rungumi kirkire-kirkire domin dacewa a wannan karni na 21, yana mai jaddada cewa dole ne jami’o’i su tashi daga zama jami’o’in da ke ba da digiri na farko su zama jiga-jigan kere-kere da fasaha da ci gaban kasa.

Farfesa Ribadu ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake gabatar da sakon fatan alheri a taron jama’a karo na hudu na Makarantar Tattalin Arziki ta Afirka (ASE), Abuja, wanda Farfesa Moses Ochonu na Jami’ar Banderbilt ta Amurka ya gabatar.

  • Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
  • Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Babban Sakatare, wanda Daraktan ci gaban fasaha da kasuwanci na NUC, Mista Ashafa Ladan, ya wakilta, ya bayyana cewa jami’o’in Nijeriya na karni na 21, “kamar Makarantar Koyon Tattalin Arziki ta Afirka, Jami’ar Pan-African of Edcellence, dole ne su sha bamban da na magabata na karni na 20, yana mai karawa da cewa dole ne su zama “cibiyar bullo da sabbin dabaru da warware matsalolin duniya.”

ADVERTISEMENT

Farfesa Ribadu ya ce waDanda suka kammala karatun jami’o’in Nijeriya “dole ne su kasance masu nutsuwa, masu sana’a, da kuma da’a yayin da binciken da ke fitowa daga jami’o’i, ba wai kawai su sanar da binciken ba, har ma su ba da gudummawa ga ci gaban kasa, ci gaban fasaha da kyautata zamantakewa.

A cikin sakon fatan alherinsa, Sakatare-Janar na Kwamitin Mataimakin Shugaban Jami’o’in Nijeriya (CBCNU), Farfesa Andrew Haruna, ya yaba wa Mataimakin Shugaban ASE, Farfesa Mahfouz Adedimeji da ma’aikatar don “yunkurinsu na ci gaba da bunkasa ilimi.”

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Ya yi nuni da cewa, jami’o’i na cikin tsaka mai wuya wajen samun sauye-sauye a duniya cikin sauri da kuma bukatu na cikin gida, wanda ke bukatar lallai sai sun sake yin nazari sosai kan tsarinsu, da dabi’unsu, domin samar da ingantaccen muradun al’ummarmu da nahiyarmu.

Ya kuma jaddada mahimmancin hangen nesa inda jami’o’i za su zama matattarar kirkire-kirkire, masu inganci da kawo sauyi a zamantakewar al’umma.

“Bari in yaba wa Makarantar Tattalin Arziki ta Afirka saboda himma da hangen nesa, ASE ta riga ta nuna kyakkyawar manufa wajen inganta karfin matasan Afirka da daidaita manyan makarantu tare da bukatun juyin-juya halin masana’antu na hudu,” in ji shi.

A cikin laccarsa mai taken, “Jami’ar Nijeriya ta Karni na 21: Matsaloli da Hanyoyi”, Babban Bako mai jawabi, Farfesa Ochonu, ya bukaci jami’o’in Nijeriya da su rungumi sauye-sauye, hade da bangarori daban-daban da kuma kusantar ilimantarwa don ci gaba da kasancewa masu dacewa a cikin kalubalen karni na 21.

A cewarsa, jami’o’i a duk fadin duniya suna fuskantar kalubale da yawa yayin da tattalin arzikin duniya ke rugujewa a karkashin tasirin juyin juya halin fasaha da na dijital a cikin ilimi, bincike da koyo. Jami’o’in Nijeriya, in ji shi, ba a cire su daga wadannan matsi ba.

Farfesa Ochonu ya yi Allah wadai da rushewar ka’idojin ilimi mai zurfi a wasu jami’o’in gwamnati wanda hakan ya sanya su zama “appendages of parochial serbices of edclusibity” yana mai cewa ana maye gurbin ilimin jama’a ta hanyar ilimin kimiyya.

Yayin da yake tabbatar da cewa fafutukar da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta yi ta tsawon shekaru ta samu wasu muhimman mutane a wuraren aiki na ilimi, ya kuma bayyana cewa gwagwarmayar ta kuma zama wani bangare na matsalar, inda ya kara da cewa “malamai da dama na ci gaba da tsallake karatu, rashin kulawa da horar da daliban jami’o’i da dama sun dage, ba a ci gaba da koyar da dalibai da yawa.”

Ya ba da shawarar Dokar Hakkin dalibi don kare dalibai a cikin alakar ilimi, kulawa, da jagoranci tare da malamai.

Farfesa Ochonu ya kuma ba da kwarin guiwa wajen sabunta sana’ar koyarwa, inda ya jaddada cewa kamata ya yi jami’o’i su kafa cibiyoyin koyarwa da kuma bayar da lambobin yabo don nagartar koyarwa domin inganta koyarwa.

Malamin da ya lashe lambar yabo ya kuma bayar da shawarar samar da tsarin da zai bai wa kwararru da ma’aikata a cikin al’umma damar samun sabbin fasahohi, kwarewa a fannoni masu tasowa da kuma gamsar da sha’awarsu ta hanyar yin rajista guda daya tare da jaddada bukatar sake fasalin manhaja.

NUC
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.