ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

by Rabi'u Ali Indabawa
11 months ago
NUC

Sakataren Zartarwa na Hukumar Kula da Jami’o’i ta Kasa (NUC), Farfesa Abdullahi Yusuf Ribadu, ya bukaci jami’o’in Nijeriya da su rungumi kirkire-kirkire domin dacewa a wannan karni na 21, yana mai jaddada cewa dole ne jami’o’i su tashi daga zama jami’o’in da ke ba da digiri na farko su zama jiga-jigan kere-kere da fasaha da ci gaban kasa.

Farfesa Ribadu ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake gabatar da sakon fatan alheri a taron jama’a karo na hudu na Makarantar Tattalin Arziki ta Afirka (ASE), Abuja, wanda Farfesa Moses Ochonu na Jami’ar Banderbilt ta Amurka ya gabatar.

  • Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
  • Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Babban Sakatare, wanda Daraktan ci gaban fasaha da kasuwanci na NUC, Mista Ashafa Ladan, ya wakilta, ya bayyana cewa jami’o’in Nijeriya na karni na 21, “kamar Makarantar Koyon Tattalin Arziki ta Afirka, Jami’ar Pan-African of Edcellence, dole ne su sha bamban da na magabata na karni na 20, yana mai karawa da cewa dole ne su zama “cibiyar bullo da sabbin dabaru da warware matsalolin duniya.”

ADVERTISEMENT

Farfesa Ribadu ya ce waDanda suka kammala karatun jami’o’in Nijeriya “dole ne su kasance masu nutsuwa, masu sana’a, da kuma da’a yayin da binciken da ke fitowa daga jami’o’i, ba wai kawai su sanar da binciken ba, har ma su ba da gudummawa ga ci gaban kasa, ci gaban fasaha da kyautata zamantakewa.

A cikin sakon fatan alherinsa, Sakatare-Janar na Kwamitin Mataimakin Shugaban Jami’o’in Nijeriya (CBCNU), Farfesa Andrew Haruna, ya yaba wa Mataimakin Shugaban ASE, Farfesa Mahfouz Adedimeji da ma’aikatar don “yunkurinsu na ci gaba da bunkasa ilimi.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Ya yi nuni da cewa, jami’o’i na cikin tsaka mai wuya wajen samun sauye-sauye a duniya cikin sauri da kuma bukatu na cikin gida, wanda ke bukatar lallai sai sun sake yin nazari sosai kan tsarinsu, da dabi’unsu, domin samar da ingantaccen muradun al’ummarmu da nahiyarmu.

Ya kuma jaddada mahimmancin hangen nesa inda jami’o’i za su zama matattarar kirkire-kirkire, masu inganci da kawo sauyi a zamantakewar al’umma.

“Bari in yaba wa Makarantar Tattalin Arziki ta Afirka saboda himma da hangen nesa, ASE ta riga ta nuna kyakkyawar manufa wajen inganta karfin matasan Afirka da daidaita manyan makarantu tare da bukatun juyin-juya halin masana’antu na hudu,” in ji shi.

A cikin laccarsa mai taken, “Jami’ar Nijeriya ta Karni na 21: Matsaloli da Hanyoyi”, Babban Bako mai jawabi, Farfesa Ochonu, ya bukaci jami’o’in Nijeriya da su rungumi sauye-sauye, hade da bangarori daban-daban da kuma kusantar ilimantarwa don ci gaba da kasancewa masu dacewa a cikin kalubalen karni na 21.

A cewarsa, jami’o’i a duk fadin duniya suna fuskantar kalubale da yawa yayin da tattalin arzikin duniya ke rugujewa a karkashin tasirin juyin juya halin fasaha da na dijital a cikin ilimi, bincike da koyo. Jami’o’in Nijeriya, in ji shi, ba a cire su daga wadannan matsi ba.

Farfesa Ochonu ya yi Allah wadai da rushewar ka’idojin ilimi mai zurfi a wasu jami’o’in gwamnati wanda hakan ya sanya su zama “appendages of parochial serbices of edclusibity” yana mai cewa ana maye gurbin ilimin jama’a ta hanyar ilimin kimiyya.

Yayin da yake tabbatar da cewa fafutukar da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta yi ta tsawon shekaru ta samu wasu muhimman mutane a wuraren aiki na ilimi, ya kuma bayyana cewa gwagwarmayar ta kuma zama wani bangare na matsalar, inda ya kara da cewa “malamai da dama na ci gaba da tsallake karatu, rashin kulawa da horar da daliban jami’o’i da dama sun dage, ba a ci gaba da koyar da dalibai da yawa.”

Ya ba da shawarar Dokar Hakkin dalibi don kare dalibai a cikin alakar ilimi, kulawa, da jagoranci tare da malamai.

Farfesa Ochonu ya kuma ba da kwarin guiwa wajen sabunta sana’ar koyarwa, inda ya jaddada cewa kamata ya yi jami’o’i su kafa cibiyoyin koyarwa da kuma bayar da lambobin yabo don nagartar koyarwa domin inganta koyarwa.

Malamin da ya lashe lambar yabo ya kuma bayar da shawarar samar da tsarin da zai bai wa kwararru da ma’aikata a cikin al’umma damar samun sabbin fasahohi, kwarewa a fannoni masu tasowa da kuma gamsar da sha’awarsu ta hanyar yin rajista guda daya tare da jaddada bukatar sake fasalin manhaja.

NUC
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.