• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC

by Abubakar Sulaiman
2 months ago
in Manyan Labarai
0
Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da fafutukar neman nasara a zaɓen shekarar 2027 ke ɗaukar zafi, bayan ƙaddamar da shugabancin riƙon ƙwarya na shugabancin jam’iyyar ADC a matakin ƙasa, magoya bayan jam’iyyar PDP da wasu jam’iyyun adawa sun fara komawa sabuwar jam’iyyar adawa ta haɗaka a jihar Borno.

Fitattun ƴan siyasa daga jam’iyyun adawa sun bayyana ADC a makon da ya gabata a matsayin sabon dandalin haɗin gwuiwa don ƙalubalantar shugaban ƙasa Bola Tinubu da jam’iyyarsa ta APC a babban zaɓen 2027.

  • ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027
  • ‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

Wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta ya nuna tsohon ɗan takarar gwamna a PDP kuma jigo a APC, Mattawali Kashim Ibrahim Imam, yana karɓar baƙuncin wasu manyan ƴan siyasa a gidansa da ke Maiduguri, inda aka bayyana cewa sun tattauna batun sauya sheƙa zuwa ADC.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa manyan ƴan adawan Nijeriya guda biyu — Alhaji Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na Labour Party — sun nuna goyon baya ga sabon dandalin siyasa na ADC. Sai dai gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya musanta raɗe-raɗin cewa shi da wasu gwamnoni guda biyar za su fice daga APC zuwa sabuwar jam’iyyar haɗaka.

Rahotannin sun nuna cewa Idris Mamman Durkwa, tsohon ɗan takarar gwamna, da Hon. Sheriff Banki, wani fitaccen matashi mai samun goyon bayan jama’a, sun jagoranci ficewar dubban mambobi daga PDP zuwa ADC.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Sannan kuma akwai Hon. Mohammed Umara Kumalia, tsohon jagoran ƴan adawa a Majalisar Wakilai; Alhaji Saleh Kida, mataimakin ɗan takarar gwamna na PDP a 2023; da Hon. Abdulrazaq Ahmed Zanna, ɗan takarar majalisa daga Bama, Ngala, da Kala Balge, da dama daga cikin tsofaffin ‘yan takara da shugabannin jam’iyyar da suka fice daga PDP da APC.

A cewar Hon. Banki, wannan babban sauyi da ake gani a jihar Borno na nuna gajiya da gazawar gwamnatin APC a matakin ƙasa da jiha. Ya caccaki shugabancin PDP na jihar ƙarƙashin Hon. Zanna Gadama da cewa sun miƙa wuya ga “matsin lamba daga sama,” wanda hakan ya haifar da ficewar mambobi masu yawa. Ya kuma ce tsadar rayuwa da rashin tsaro sun ƙara jefa mutane cikin ƙunci, wanda hakan ya sa jama’a ke neman mafita daga irin wannan jagoranci.

Ya buƙaci jama’ar jihar su marawa ADC baya, yana mai bayyana ta a matsayin jam’iyyar da za ta dawo da dimokuraɗiyya ta gari tare da ceto al’ummar Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ADCAPCBornoPDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Taron Layin Dogo Mai Saurin Gudu Na Duniya Karo Na 12 A Beijing

Next Post

Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

Related

Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

8 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

10 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

13 hours ago
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

19 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

1 day ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

2 days ago
Next Post
Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.